| Hausa
TURKIYYA
3 minti karatu
Daƙile yunƙurin juyin mulki na 2016 ya 'bayyana 'yancin kai' na ƙarni ga Turkiyya, in ji Erdogan
A wani saƙo da ya wallafa a ranar 15 ga Yuli na cika shekaru 10 da yunƙurin juyin mulki da bai yi nasara ba a Turkiyya, Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya ce Turkiyya ta fito ƙarara ta ƙara haɗin kai da jajircewa a yaƙin da take yi da FETO.
Daƙile yunƙurin juyin mulki na 2016 ya 'bayyana 'yancin kai' na ƙarni ga Turkiyya, in ji  Erdogan
Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya bayyana cewa ranar 15 ga watan Yuli babbar nasara ce ga dimokuradiyya a ƙasar

Shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana yunƙurin juyin mulki na ranar 15 ga Yuli, 2016 da bai yi nasara ba a matsayin wani muhimmin lokaci a tarihin ƙasar, inda ya kira shi a matsayin "'yancin kai" na ƙarni ga Turkiyya.

A wata muƙala mai taken 15 ga Yuli: Samun 'yancin kai na ƙarni ga Turkiyya, wadda aka wallafa don bikin cika shekaru 10 a tsarin Dimokuraɗiyya da kuma Ranar Haɗin Kan Ƙasa, Erdogan ya ce juyin mulkin da bai yi nasara ba wanda Ƙungiyar Ta'addanci ta Fetullah (FETO) ta shirya ba kawai yunƙurin kifar da gwamnati ba ne, har ma da hari ga 'yancin kai da kuma ƙudurin dimokuraɗiyya na ƙasar.

"Ranar 15 ga Yuli ba wai kawai dare ne da aka daƙile wani yunƙuri na juyin mulki mai cike da ruɗani ba, babbar nasara ce ga dimokuraɗiyya, wadda aka rubuta da haruffan zinare a tarihi, a daidai lokacin da al'ummarmu ke kare muradu, dimokuraɗiyya da kuma 'yancin kai wanda ya jawo asarar rayuka da dama," in ji shi.

An kashe mutane 253 tare da jikkata fiye da 2000

Erdogan ya ce al'ummar Turkiyya sun amsa kiransa na fitowa kan tituna da irin jajircewar da aka nuna a yaƙin neman 'yancin kai na ƙasar, inda ya ƙara da cewa an kashe mutane 253 kuma an jikkata fiye da 2000 yayin da suke adawa da yunƙurin juyin mulkin.

Ya ce kiransa ga jama'a da su nuna turjiya ya nuna ƙarfin gwiwarsa ga “hikimar dimokuraɗiyyar ƙasar, da hangen nesa, da kuma jarumtarta.”

A yayin da yake waiwaiye bayan yunƙurin juyin mulkin, Erdogan ya ce hukumomi sun bi sahun yaƙi da ƙungiyar FETO a ciki da wajen Turkiyya.

“Mun kawar da FETO daga kowane fanni, tun daga cikin gwamnati da sojoji zuwa ɓangaren shari'a da ‘yankasuwa," in ji shi, yayin da ya jaddada cewa yaƙin bai ƙare ba.

"Hanya ɗaya tilo da za a iya hana ƙungiyar FETO da ire-irenta daga yin kutse ko shiga ƙasarmu ita ce a ci gaba da rayuwa da ruhin ranar 15 ga watan Yuli tare da wayar da kan jama'a musamman al’ummar gaba, " in ji shi.

‘Turkiyya ta ƙara ƙarfi a cikin shekaru nan da suka wuce’

“Muna ci gaba da yaƙi da FETO da duk wasu ƙungiyoyin ta'addanci masu iri wannan ƙuduri. A juyayin cika shekaru 10 na ranar 15 ga Yuli, Turkiyya ta ƙara ƙarfi, tare da samun haɗin kai,” in ji shi.

“Muddin ruhin ranar 15 ga Yuli ya ci gaba da wanzuwa a wannan ƙasa, kar wani ya yi shakkar cewa shirye-shiryen maciya amana da kuma munanan matakan da waɗanda suka kitsa juyin mulkin a duniya ba za su taɓa yin nasara ba,” in ji shi.

Kazalika Shugaba Erdogan ya jinjina wa shahidan da aka kashe a lokacin yunƙurin juyin mulkin da kuma addu'ar Allah ya dawwamar da haɗin kan Turkkiyya.

Rumbun Labarai
Jami’an leƙen asiri na Turkiyya sun kama wani babban jami’in Daesh a Syria
Manufofi da gwamnatin Netanyahu 'nauyi' ne ga Isra'ila da yankin da tsaron duniya: Ministan Turkiyya
Emine Erdogan ta karbi bakuncin matan shugabannin NATO don tattaunawa kan yara, fasaha da tsaro
Shugaba Erdogan ya ce taron NATO a Ankara ‘nasara ce ta tarihi’
Taron Trump-Erdogan: Amurka za ta ɗage wa Turkiyya takunkumai, za a yanke hukunci kan F-35 nan kusa
Tsaron Turai ba zai ta’allaka ga Tarayyar Turai ba, in ji Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan
Taron Koli na NATO a Ankara na nuna muhimmiyar rawar Turkiyya a harkar tsaro da diflomasiyyar duniya
Muhimmin labarin fursunonin yaki Turkawa da ya sauya fasalin aƙidun horon sojojin NATO
Turai za ta yi amfani da taron NATO a Ankara ta nuna wa Trump kyakkyawar niyyarta kan tsaro: Jamus
Shugaban Turkiyya Erdogan ya karɓi baƙuncin Firaministan Pakistan Sharif a Istanbul
Salon Turkiyya na sasanci da taimakon tsaro yana inganta harkar tsaro a Afirka
Yadda Turkiyya ke ƙarfafa rawar da take takawa a NATO kafin babban taron ƙawance a Ankara
Shugaba Erdogan ya soki Isra'ila game da gangamin ɓata suna da ƙarairayi kan Turkiyya
Tawagar majalisar dokokin NATO ta ziyarci kamfanin Baykar mai ƙera jirage marasa matuƙa a Ankara
Taron NATO na Ankara zai kasance "babban dandali mai ƙarfi na musayar ƙwarewa: Erdogan na Turkiyya
Mataimakin Shugaban Kasar Turkiyya na neman a bunkasa kasuwanci a tsakanin duniyar Musulunci
Ma'aikatan agajin Turkiyya sun fara aikin ceto a Venezuela bayan girgizar ƙasa
Turkiyya ta tura tawagar bincike da ceto zuwa Venezuela bayan iftila'in tagwayen girgizar kasa
Shugaban Turkiyya da na Mauritaniya sun tattauna dangantaka tsakanin ƙasashensu da batutuwan yanki
'Ankara za ta ƙara ɗaukaka a diflomasiyyar duniya ta hanyar karbar tarukan NATO da ƙasashen Turkawa'