NIJERIYA
2 minti karatu
Abu biyar da ministocin harkokin wajen Nijeriya da Nijar suka tattauna a kai
Daga cikin abubuwan da ministocin Nijeriya da Nijar suka tattauna har da batun gina babbar hanyar mota wadda za ta ratsa ta cikin sahara domin inganta sufuri a tsakanin ƙasashen.
00:00
Abu biyar da ministocin harkokin wajen Nijeriya da Nijar suka tattauna a kai
A tattaunawar da Yusuf Tuggar ya yi da takwaransa na Nijar Bakary Yaou Sangare, sun yi nazari kan irin ƙalubalen da ƙasashen ke fuskanta.
17 Afrilu 2025

Ministocin harkokin wajen Nijeriya da Nijar sun gudanar da wata tattaunawa game da tsaron kan iyaka da ta’addanci da haɗin kan tattalin arziki a daidai lokacin da ake ci gaba da zaman ɗarɗar tsakanin maƙwabtan biyu tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a Nijar a watan Yulin 2023.

Wannan tattaunawar na zuwa ne bayan a watan nan Nijeriya ta ci gaba da kira ga gwamnatin Nijar ta saki Shugaba Mohamed Bazoum, wanda aka yi wa ɗaurin-talala a fadar shugaban ƙsasar ta Nijar.

Ziyarar da Ministan Harkokin Wajen Nijeriya Yusuf Tuggar ya kai Yamai ita ce ta biyu da wani babban jami’in Nijeriya ya kai ƙasar bayan juyin mulki a ƙasar inda a kwanakin baya babban hafsan tsaron Nijeriya Christopher Musa ya kai irin wannan ziyara a watan Agusta.

A tattaunawar da Yusuf Tuggar ya yi da takwaransa na Nijar Bakary Yaou Sangare, sun yi nazari kan irin ƙalubalen da ƙasashen ke fuskanta.

Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan barazanar ta'addanci a kan iyakokinsu, "wanda ke zama babban cikas ga aiwatar da dukkanin shirye-shiryen ci gaba mai inganci", in ji sanarwar.

Dangane da haɗin gwiwa ta ɓangaren tattalin arziki, ministocin sun tattauna kan aikin layin dogo da zai haɗa garuruwan Kano da Katsina na Nijeriya zuwa Maraɗi a Nijar, wanda ake sa ran za a ƙaddamar a 2026.

Haka kuma sun tattauna kan batun gina babbar hanyar mota wadda za ta ratsa ta cikin sahara, da kuma aikin gina bututun mai wanda zai ratsa ta cikin sahara.

Haka kuma ministocin sun tattauna kan batun jami’ansu na kwastam da batun karɓar haraji.

Ƙasashen Nijar da Burkina Faso da Mali sun fice daga ƙungiyar tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka a farkon wannan shekara, inda suka zargi ECOWAS da gazawa wajen yaƙi da ƙungiyoyin 'yan ta'adda. Ƙasashe uku ƙarƙashin jagorancin soja sun kafa nasu ƙawancen na ƙasashen Sahel.

Rumbun Labarai
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya
Tinubu ya mayar da martani bayan Amurka ta ce ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada aniyarta ta yaƙi da tsattsauran ra'ayi
Samaila Bagudo: 'Yan bindiga sun sace Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kebbi
Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla