| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Bankin Duniya zai tallafa wa Nijar da dala miliyan 250 don taimakon bankuna da ƙananan ‘yan kasuwa
A cewar Bankin Duniya, shirin zai taimaka wa cibiyoyin kudi su ci gaba da bayar da rance ga ‘yan kasuwa sannan ya kuma taimaka wajen samar da ayyukan yi da ƙarin hanyoyin samun kuɗin shiga ga jama’a.
Bankin Duniya zai tallafa wa Nijar da dala miliyan 250 don taimakon bankuna da ƙananan ‘yan kasuwa
Firaministan Nijar Ali Mahamane Lamine ZEINE
15 Maris 2026

Bankin Duniya ya amince da bayar da tallafin dala miliyan 250 domin taimakawa wajen farfado da ɓangaren kuɗi a Nijar tare da inganta damar samun jari ga ƙanana da matsakaitan sana’o’i.

Tallafin, wanda aka amince da shi a ranar 12 ga Maris na 2026, ya fito ne daga International Development Association wadda ke ƙarƙashin Bankin Duniya, kuma ana sa ran tallafi zai taimaka wajen dawo da isassun kudi a bankuna tare da ƙarfafa bankuna su sake bai wa ƙanana da matsakaitan ‘yan kasuwa bashi a faɗin kasar.

A cewar Bankin Duniya, shirin zai taimaka wa cibiyoyin kudi su ci gaba da bayar da rance ga ‘yan kasuwa sannan ya kuma taimaka wajen samar da ayyukan yi da ƙarin hanyoyin samun kuɗin shiga ga jama’a.

Tattaunawa kan wannan shiri ta ɗauki watanni da dama, kuma an sake duba ta a ƙarshen watan Janairu a yayin ganawar Firaministan Nijar, Ali Mahamane Lamine Zeine, da wata tawaga daga Bankin Duniya karkashin jagorancin wakilin bankin a Nijar, Affouda Léon Biaou.

Ana sa ran shirin zai taimaka wa kimanin ƙanana da matsakaitan sana’o’i 7,500, ciki har da kasuwancin da mata ke jagoranta da kuma ayyukan da ke jure sauyin yanayi, tare da taimakawa wajen ƙirƙira ko kuma ci gaba da riƙe kusan ayyukan yi 58,000.

Bangaren kuɗi na Nijar ya fuskanci matsin lamba tun bayan rikicin siyasa na watan Yulin 2023, wanda ya janyo takunkumin tattalin arziki daga ƙasashen yankin, lamarin da ya jefa bankuna da cibiyoyin bada rancen kuɗi cikin matsalar rashin isasshun kudi.

Bankin Duniya ya ce wannan matsala ta rage ƙarfin bankuna wajen bai wa ‘yan kasuwa rance, musamman ƙanana da matsakaitan sana’o’i da ke buƙatar jari domin ci gaba da gudanar da harkokinsu da bunkasa kasuwanci.

Jami’in ayyuka na Bankin Duniya a Nijar, Johan A. Mistiaen, ya ce shirin zai taimaka wajen buɗe sabbin damammaki ga ‘yan kasuwar Nijar.

Shirin zai kuma hada da taimakon fasaha ga cibiyoyin kuɗi da kuma wani shiri na gaggawa domin ba da damar ɗaukar matakan hanzari idan wata matsala ta sake tasowa nan gaba.

Rumbun Labarai
Dalilin da ya sa Kenya da Ethiopia suka zama manyan masana'antun furanni a duniya
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 15 a Angola
Senegal ta haramta wa jami'an gwamnati tafiye-tafiye marasa muhimmanci zuwa ƙasashen waje
Yadda aikin dala miliyan 240 ke bai wa al’umar gaɓar teku a Benin da Mauritania damar gwagwarmaya
Gwamnatin Madagascar ta daƙile yunƙurin kashe shugaban ƙasar Michael Randrianirina
Sudan ta yi Allah wadai da 'mummunan' harin da RSF ta kai wani asibiti yayin allurar rigakafin yara
Ghana za ta fara aiwatar da shirin shiga ƙasar ba tare da biza ba ga dukkan 'yan Afirka
Shugaban riƙon jihar Kudu maso yammacin Somaliya zai hau kan mulki bayan ajiye aikin shugaba
Sudan ta nemi 'yan ƙasar da suka yi ƙaura zuwa ƙasashen waje saboda yaƙi su koma gida
Hukumar leƙen asirin Somalia ta kashe masu haɗa bama-baman Al Shabab
Mali ta musanta rahoton sakin ’yanta’adda 200 domin samun man fetur
An kasa cim ma matsaya kan sabbin sauye-sauye a tattaunawar WTO a Kamaru
Darasin da Togo ke koya wa sauran kasashe wajen magance cututtukan da aka yi watsi da su
’Yanbindiga sun kashe fararen-hula 16 kusa da iyakar Nijar da Mali
Nijar ta ƙaddamar da sabon katin ɗan ƙasa na zamani mai tambarin AES
Laifi mafi muni: AU ta nemi MƊD ta ɗauki mataki kan biyan diyyar cinikin bayi bayan MƊD ta tabbatar
Ghana ta sake yin bita kan tsarin yaƙi da ta’addanci sakamakon barazanar masu tsattsauran ra’ayi
Rasha ta yi iƙirarin cewa 'yan kwangilar sojin Faransa na da yawa a Afirka
Hukumomi a Nijar sun kama wani mutum a Zinder bisa zargin yawan kai wa 'mata' hari a kan babur
Me ya sa diyyar cinikin bayi da mulkin mallaka suka zama masu muhimmanci ga Afirka a 2026