AFIRKA
2 minti karatu
Sojojin da suka yi juyin mulki a Madagascar sun ce a shirye suke su tattauna da Tarayyar Afirka
"Ba mu yi mamakin matakin da aka ɗauka ba. (Amma) daga yanzu, za mu yi tattaunawar sulhu ta bayan-fage. Za mu ga yadda za ta kaya," in ji Kanar Michael Randrianirina.
Sojojin da suka yi juyin mulki a Madagascar sun ce a shirye suke su tattauna da Tarayyar Afirka
Randrianirina ya ce zai sha rantsuwar kama aiki ranar Jumma'a a gaban kotun kundin tsarin mulki ta ƙasar
17 Oktoba 2025

Jagoran sojojin da suka yi juyin mulki a Madagascar, Kanar Michael Randrianirina, ya ce a shirye yake ya tattauna da ƙungiyar Tarayyar Afirka, wadda ta dakatar da ƙasar daga cikinta saboda kifar da gwamnatin Andry Rajoelina.

"Ba mu yi mamakin matakin da aka ɗauka ba. (Amma) daga yanzu, za mu yi tattaunawar sulhu ta bayan-fage. Za mu ga yadda za ta kaya," in ji Kanar Michael Randrianirina a wani taron manema labarai da ya jagoranta ranar Alhamis.

Randrianirina ya ce zai sha rantsuwar kama aiki ranar Jumma’a a gaban Babbar Kotun Tsarin Mulki ta ƙasar a Antananarivo, babban birnin ƙasar.

Sai dai a ranar Alhamis, Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres ya yi Allah wadai da juyin mulkin da sojoji suka yi wa gwamnatin farar-hula a ƙasar, inda ya yi kira a dawo da tsarin mulki da doka.

"Ina yin tir da kawar da gwamnati da ƙarfin soji a Madagascar kuma ina kira a dawo da tsarin mulki da doka," a cewar Guterres a wata sanarwa da ya wallafa.

"Ina bayar da shawara ga dukkan masu rua da tsaki na Malagascar, ciki har da matasa su yi aiki tare domin magance matsalolin da suka haddasa yamutsi a ƙasar," in ji shi.

Ya ƙara da cewa a shriye MDD take ta yi aiki tare da ‘yan ƙasar da kuma neman goyon bayan ƙasashen duniya domin maido da tsarin mulki da oda.

Rajoelina, wanda ‘yan majalisar dokokin ƙasar suka tsige bayan ya tsere daga ƙasar, inda ya nuna fargaba game da yiwuwar halaka shi sakamakon zanga-zangar da matasa suka kwashe makonni suna yi wadda sojoji suka goyi bayanta, ya soki matakin Randrianirina na ɗarewa karagar mulki ƙasar.

Rumbun Labarai
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya
Dubban mutane sun tsere daga North Kordofan yayin da RSF ta zafafa kai hari a yankin Darfur na Sudan
Fararen-hula 177,000 sun maƙale a Al Fasher na Sudan, yayin da RSF ke ci gaba da kisa - Likitoci