| Hausa
SIYASA
2 minti karatu
Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara a Nijeriya ya fice daga PDP zuwa APC
Gwamnan Jihar Zamfara a Nijeriya, Dauda Lawal ya sanar da ficewarsa daga Jam’iyyar zuwa jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar, sakamakon rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar.
Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara a Nijeriya ya fice daga PDP zuwa APC
Dauda Lawal / Others
16 awanni baya

Gwamnan Jihar Zamfara a Nijeriya, Dauda Lawal ya sanar da ficewarsa daga Jam’iyyar zuwa jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar, sakamakon rikicin cikin gida da ya dabaibaye jam’iyyar.

An sanar da wannan mataki ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a ranar Litinin a dakin taro na Rescue Hall da ke Gidan Gwamnatin jihar a Gusau. Mataimakin gwamnan jihar, Mani Mummuni, ne ya jagoranci taron, inda shugabannin siyasa da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar suka halarta.

Da yake magana a madadin gwamnan, mataimakin gwamnan ya ce an dauki wannan mataki ne bayan shawarwari masu zurfi da kuma duba halin da jam’iyyar PDP ke ciki.

“Bayan sauraron shawarwarinku da yin nazari mai zurfi, musamman bukatar samun hadin kai a tsakanin manyan ‘yan siyasa domin magance matsalolin tsaro a jihar, Mai Girma Gwamna Dauda Lawal ya yanke shawarar komawa jam’iyyar APC,” in ji shi.

Ya kuma umarci dukkan masu rike da mukaman siyasa da ke goyon bayan gwamnan da su gaggauta ajiye mukamansu na PDP, su kuma shirya yin rajista da APC da zarar an sake bude rajistar ta intanet.

A cewarsa, shugabancin siyasar jihar na da burin kara rajistar sabbin mambobin APC har 400,000 a cikin kwanaki 17 masu zuwa a jihar.

Wannan mataki ya biyo bayan wasu shawarwari da tuntuɓa na jiha baki daya da Gwamna Lawal ya kaddamar a watan Janairu domin tantance makomar siyasar jihar, a daidai lokacin da rikicin PDP ke kara tsananta, tare da la’akari da shirye-shiryen babban zaben 2027.

Gwamna Lawal ya kuma gode wa jam’iyyar PDP bisa damar da ta ba shi na tsayawa takarar gwamna a zaben 2023, inda ya ce ya yi kokari wajen sasanta rikicin cikin gida na jam’iyyar, amma hakan bai yi nasara ba.

Ya kuma gode wa al’ummar Zamfara bisa goyon baya da kaunar da suke nuna masa, tare da tabbatar musu cewa manufar gwamnatinsa ta “Rescue Agenda” za ta ci gaba da tafiya yadda aka tsara duk da sauyin jam’iyyar.