Wane ne Franck Biya da ake hasashen zai iya Shugaban Ƙasar Kamaru na gaba?
SIYASA
3 minti karatu
Wane ne Franck Biya da ake hasashen zai iya Shugaban Ƙasar Kamaru na gaba?Ana ci gaba da muhawara a tsakanin 'yan Kamaru game da yiwuwar samun sauyin shugabanci daga Biya babba zuwa Biya ƙarami da kuma tasirin da hakan zai haifar.
Franck Biya, ɗan shugaban ƙasar Kamaru yayi da je ƙaddamar da yakin takarar shugaban ƙasa na mahaifinsa a watan Oktoban 2025. / Reuters

Batun siyasa da shugabancin Kamaru sun sake janyo zazzafar muhara.

Suna ɗaya da ake yawan ambatowa a kafafen yada labarai shi ne Franck Emmanuel Biya, wato ɗan shugaban ƙasar Paul Biya da ya daɗe a kan mulki.

A 'yan kwanakin nan, kafafen yada labarai daban-daban na gida a ƙasashen Afirka, ciki har da na Kamaru, sun ba da rahoton cewa an naɗa Franck a matsayin mataimakin shugaban ƙasar kana shi zai gaji mahaifinsa a matsayin shugaban ƙasar na gaba.

Rahotannin, waɗanɗa suka nakalto wani kwafin umarnin shugaban kasa da aka fitar mai ɗauke da kwanan 4 ga watan Afrilun 2026, sun ce Franck zai jagorancin shugabancin rundunar sojin kasar tare da yin aiki a matsayin "Wakilin Minista" a Ma'aikatar Tsaro.

Kawo yanzu dai gwamnatin Kamaru ba ta tabbatar ko musanta rahotannin kafofin watsa labarai da aka yaɗa ba.

An dawo da kujerar mataimakin Shugaban Ƙasa

Majalisar Dokokin Ƙasar ta dawo da kujerar mataimakin shugaban ƙasa a makon da ya gabata, bayan shafe fiye da shekaru 50 da soke matsayin.

Dokar da ta dawo da matsayin ta tanadi cewa mataimakin shugaban ƙasa zai zama shugaban ƙasa kai tsaye idan shugaban ya mutu, ko ya yi murabus ko kuma ya rasa ƙarfinsa har abada.

Yayin da wasu masu sharhi ke cewa, akwai yiwuwar dokar an kafa ta ne a matsayin wata dabara ta tabbatar da cewa mataimakin da Paul Biya ya zaɓa shi zai gaje shi, matakin da jami'an gwamnati suka ce yana da nufin tabbatar da "tsaron cigaban gwamnati".

Paul Biya wanda ya hau mulki tun daga shekarar 1982, a halin yanzu shi ne shugaban ƙasa mafi tsufa a kan mulki a duniya yana da shekaru 93 kuma a wa’adin mulkinsa na takwas bayan zaɓen shugaban ƙasa na watan Oktoba.

Ɗansa, Franck Emmanuel Biya, wanda yana cikin waɗanda ake hasashen za su iya maye gurbinsa, ba a cika jin duriyarsa ba a tsawon shekaru, haka kuma ba a saba ganinsa a cikin harkokin siyasa ko mukamai na gwamnati ba.

Ɗankasuwa ne. An haife shi a 1971, kuma Franck shi ne babban ɗan Shugaba Paul Biya.

Mahaifiyarsa ita ce Jean-Irène Biya, matar Shugaba Biya ta farko, wacce ta mutu a shekarar 1992.

Franck ya yi karatu a Kamaru kafin ya koma Amurka, inda ya kammala karatunsa na digiri a fannin Kimiyyar Siyasa da Tattalin Arziki daga Jami'ar Kudancin California a shekarar 1994.

Sannan ya yi aiki a Bankin Kasashen yankin Tsakiyar Afirka sannan daga baya ya yi aiki a wani kamfanin gandun daji.

A shekarar 2004, ya kafa Venture Capital PLC, wani kamfani da ke dake gudanar da harkokin banki da gandun daji da kuma makamashi, inda ya mai da hankali a hannayen jari a Afirka da wasu ƙasashen waje.

Yayin da ake kan jiran sanarwa a hukumance game da nadin mataimakin shugaban ƙasa a Kamaru, ana ci gaba da muhawa a tsakanin 'yan ƙasar Kamaru game da yiwuwar sauyin shugabanci daga Biya babba zuwa Biya ƙarami da kuma tasirin da hakan zai haifar.

Rumbun Labarai
Danmajalisar Amurka na son a ƙwace shaidar ɗan ƙasa ta duk mai alaƙa da Tsaurin Ra'ayin Musulunci
Me ya sa Amurka ke komawa ga zamanin Yakin Duniya na II, da tunkarar masu motoci don kera makamai?
Ministan Kudin Benin Romuald Wadagni ya lashe zaben shugaban kasar
Wane tasiri shigar Yusuf Buhari siyasar Nijeriya za ta yi?
Rikicin cikin gida na Jam'iyyar ADC da makomar dimokuraɗiyyar Nijeriya
Sabon Salo a Siyasar Nijeriya: Nazari kan Jihar Kano
Za a ci gaba da tsare El-Rufai yayin da kotu ta ɗage sauraron buƙatar neman beli zuwa 14 ga Afrilu
Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara a Nijeriya ya fice daga PDP zuwa APC
Jam’iyyun Adawa a Nijeriya sun yi watsi da Dokar Zabe ta 2026, sun nemi a yi sabon gyara
Jajircewar Turkiyya a Afirka: Labarin haɗin-kai da kyakkyawan fata
Martanin duniya a yayin da Isra’ila ke rajistar mallake Gabar Yammacin Kogin Jordan
Shugaban Nijar ya ziyarci Aljeriya, lamarin da ya nuna ƙarshen tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen
Trump ya bar ƙofar Iran a bude, kuma Netanyahu ba zai iya rufe ta ba
Yadda 'yan Nijeriya suka fusata kan matakin Amurka na saka wa Kwankwaso takunkumi
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta Nijeriya
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Iran ta ce ta shiga tattaunawar Oman da Amurka da 'kyakkyawar niyya'
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
Greenland ba hajar sayarwa ba ce