| Hausa
DUNIYA
2 minti karatu
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
Rahoton da Cibiyar Sanya Idanu Kan Kafafen Watsa Labarai ya ce kashe 70 na makalai da ke da alaka da Musulmai ko Musulunci ba labarai masu kyau ba ne, inda masu ra’ayin rikau suka fi zafafawa.
Kusan rabin rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya kan Musulmi na dauke da nuna wariya
FILE PHOTO: Taron buda baki na 2025 da aka shirya a dandalin Trafalgar da ke Landan. / Reuters
5 awanni baya

Wani bincike da aka yi kwanan nan ya gano cewa kusan rabin dukkan rahotannin kafafen watsa labaran Birtaniya game da Musulmai na ɗauke da wani mataki na nuna son kai.

Binciken da Cibiyar Sanya idanu Kan Kafafen Watsa Labarai (CfMM) ta gudanar ya gano cewa nuna son kai ya yaɗu a faɗin kafafen Watsa labarai na Birtaniya a shekarar 2025, inda kusan kashi 50 cikin ɗari na dukkan labaran suka ƙunshi wani nau'in nuna son kai.

Rahoton ya gano cewa kusan labarai 20,000 daga cikin labarai 40,913 da aka buga a manyan gidajen watsa labarai 30 sun nuna son kai ta wata hanya.

Ya kuma bayyana cewa kashi 70 cikin ɗari na labaran sun haɗa Musulmai ko Musulunci da halaye ko matsaloli marasa kyau.

Rahoton ya bayyana kafofin watsa labarai na masu ra’ayin rikau a matsayin babban tushen nuna son kai ga Musulmai, inda The Spectator ke da mafi yawan labara masu cike da "son kai".

Sauran gidajen watsa labarai da suka fi nuna son kai ga Musulmai sun haɗa da GB News, The Telegraph, Jewish Chronicle, Daily Express, The Sun, Daily Mail da The Times.

"A matsayin babban bincike irin sa da aka taɓa yi a Birtaniya, wannan rahoton ya gabatar da hujjoji masu tayar da hankali game da nuna son kai a tsarin yadda ake nuna Musulmai a cikin jaridun Birtaniya," in ji Rizwana Hamid, darektan CfMM.

Rumbun Labarai
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba
Trevor Noah: Trump ya yi barazanar maka mai gabatarwa a Gasar Grammy a Kotu
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela