| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Majalisar Dokokin Nijeriya ta ba da shawarar yin manyan zaɓukan ƙasar a watan Nuwamban 2026
Idan har aka amince da wannan shawara, ke nan za a yi manyan zaɓukan Nijeriya wata shida kafin lokacin da aka saba yin su, wato a watan Fabrairu.
Majalisar Dokokin Nijeriya ta ba da shawarar yin manyan zaɓukan ƙasar a watan Nuwamban 2026
Shugaban Majalisar Dattijan Nijeriya Godswill Akpabio
14 Oktoba 2025

Majalisar Dokokin Nijeriya ta ba da shawarar a dawo da manyan zaɓukan ƙasar baya zuwa watan Nuwamban 2026 maimakon yin su a watan Fabrairun shekarar 2027.

An bayyana hakan ne a cikin Ƙudrin Dokar Zabe (da aka gyara) ta 2025, wadda aka gabatar yayin taron jin ra'ayin jama'a na hadin gwiwa na Kwamitocin Majalisar Dattijai da na Wakilai kan Harkokin Zaɓe da suka shirya a Abuja a ranar Litinin.

Idan har aka amince da wannan shawara, ke nan za a yi manyan zaɓukan Nijeriya wata shida kafin lokacin da aka saba yin su, wato a watan Fabrairu.

An yanke shawarar yin gyaran ne don tabbatar da cewa an kammala dukkan batutuwan da suka shafi zaɓe kafin ranar 29 ga Mayun 2027, wato lokacin miƙa mulki.

‘Yan majalisar, sun kuma bayar da shawarar ƙara ƙarfafa ɓangaren shari’a don warware matsalolin da suka shafi al’amuran zaɓe.

Sauran abubuwan da suka fi daukar hankali a cikin kudurin sun hada da bai wa fursunoni damar zaɓe, da bai wa ‘yan Nijeriya mazauna ƙsashen waje damar kaɗa ƙuri’a da wuri, da amfani da katin shaidar zama ɗan ƙasa, NIN wajen rajistar masu kaɗa ƙuri’a, da kuma miƙa sakamakon zaɓe ta intanet.

‘Yan majalisar sun ce matakin zai kawar da matsalar saye da sayar da ƙuri’a, waɗanda suka yawaita a zaɓukan da suka gabata, da kuma tabbatar da tantance masu kaɗa ƙuri’a gaba ɗaya.

Dokar Zabe (da aka gyara) ta 2025 ta ce dole ne majalisun biyu su amince da ita kafin a miƙa ta ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu domin ya amince da ita.

 

Rumbun Labarai
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
Trump ya umarci Ma'aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya