| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa
Tehran ta tsare daruruwan mutane kan zargin leƙen asiri bayan yaƙin Amurka da Isra’ila da Iran
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa
Iran ta kama mutum 127 kan zargin taya abokan gaba shirya kai mata hari ta ƙasa / Reuters

Rundunar Juyin Juya Hali ta Iran, IRGC ta sanar da kama aƙalla mutum 127 a sassa daban-daban na ƙasar, inda ta ce suna da alaƙa da Birtaniya da Amurka da kuma Isra’ila, kuma suna “taya abokan gaba shirya yadda za a kai harin soji ta ƙasa.”

A cewar kamfanin dillancin labarai na Tasnim, an kama mutum bakwai a lardin Gabashin Azerbaijan, inda aka zarge su da “shirya makamai da tsara ayyukan ɓarna, tare da aika bayanan wurare masu muhimmanci ga abokan hulɗarsu a ƙasashen waje.”

Haka kuma, an kama mutum 69 a lardin Mazandaran, yayin da aka gano wasu 51, ciki har da ƙungiyoyin leƙen asiri uku a lardin Kerman.

Tehran ta tsare mutane da dama kan zargin leƙen asiri tun bayan yaƙin da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar a kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya yi sanadin mutuwar fiye da mutane 3,000.

Sabuwar dokar leƙen asiri da aka ƙarfafa a Iran na bai wa hukumomi damar yanke hukuncin kisa ga waɗanda aka samu da laifin leƙen asiri, tare da ƙwace dukiyoyinsu.

MAJIYA:Anadolu Agency