| hausa
AFIRKA
2 minti karatu
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Wasu daga cikin 'yan matan an yi musu fyaɗe a cikin Al Fasher bayan RSF ta ƙwace garin, yayin da wasu aka ci zarafin su a lokacin da suke ƙoƙarin tserewa zuwa garin Tawila da ke maƙwabtaka, in ji Ƙungiyar Likitocin Sudan.
An samu rahotanni 32 na yi wa 'yan mata fyade bayan RSF ta ƙwace birnin Al Fasher - Likitoci
Yaƙin na Sudan tsakanin sojoji da RSF, wanda ya fara a Afrilun 2023, ya kashe aƙalla mutum 40,000 kuma ya tilasta wa mutane miliyan 12 barin gidajensu
16 Nuwamba 2025

Wata ƙungiyar likitoci ta Sudan ta bayar da rahoton fyaɗe 32 da aka yi wa ‘yan matan da ke tserewa daga Al Fasher cikin mako guda, a daidai lokacin da birnin da ke yammacin na Sudan ke ci gaba da kasancewa a hannun hannun mayaƙan ƙungiyar Rapid Support Forces (RSF).

Wasu daga cikin 'yan matan an yi musu fyaɗe a cikin Al Fasher bayan RSF ta ƙwace garin, yayin da wasu aka ci zarafin su a lokacin da suke ƙoƙarin tserewa zuwa garin Tawila da ke maƙwabtaka, in ji Ƙungiyar Likitocin Sudan a wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi.

Ta yi Allah wadai da fyaɗen a matsayin "ƙeta alfarmar ta ƙasa da ƙasa kuma yana daidai da laifukan yaki da laifukan cin zarafin bil'adama."

Sanarwar ta ce waɗannan laifuka "suna bayyana yadda rashin tsari da cin zarafi yake shafar mata da 'yan mata a wuraren da RSF ke iƙirarin iko da su, a cikin yanayin da babu kariya kuma babu wani nau'i na sa ido."

Ƙungiyar likitocin ta ɗora cikakken alhakin ga RSF kuma ta yi kira na gaggawa da a gudanar da bincike na ƙasa da ƙasa mai zaman kansa da samar da kariya nan take ga waɗanda abin ya shafa da shaidu da kuma bai wa ƙungiyoyin lafiya da na jinƙai damar shiga ba tare da takunkumi ba don samar da kulawa, magani, da shawarwarin natsar da ƙwaƙwalwa da na shari'a.

Yaƙin na Sudan tsakanin sojoji da RSF, wanda ya fara a Afrilun 2023, ya kashe aƙalla mutum 40,000 kuma ya tilasta wa mutane miliyan 12 barin gidajensu, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO).

A watan da ya gabata, RSF ta ƙwace Al Fasher, babban birnin Jihar Darfur ta Arewa, inda ake zarginta da kai hare-hare da kisan kiyashi. Kungiyar tana da iko da duka jihohin Darfur guda biyar a cikin jihohin Sudan 18, yayin da sojoji ke rike da mafi yawan sauran jihohin 13, ciki har da Khartoum.

Darfur ita ce kusan kusan ɗaya bisa biyar na yankin Sudan, amma mafi yawan mutanen ƙasar kimanin miliyan 50 suna rayuwa a yankunan da sojoji ke mulki.

Rumbun Labarai
Ghana za ta tura injiniyoyin soji don taimakawa wajen sake gina Jamaica bayan afkuwar guguwa
Mutane 70 sun ɓace bayan jirgin ruwa ɗauke da mutum 120 ya kife a DRC
Wata ƙungiya ta zargi kamfanin Nestle da sayar wa Afirka abincin jarirai mai sikari da yawa
Ranar Makewayi ta Duniya: Kundin tsafta na Afirka don inganta lafiya da mutunci
Sabon Alƙalin Alƙalan Ghana Baffoe-Bonnie ya fara aiki
An raba fiye da mutum 100,000 da gidajensu a Al Fasher na Sudan daga lokacin da RSF ta ƙwace birnin
Kafafen watsa labaran Afirka: Abokan kawo ci gaba da ake mantawa da su
Za a ƙara farashin man fetur a Ghana
Ruftawar mahaƙar ma’adanai ta yi ajalin aƙalla mutum 32 a DRC
Mutum huɗu sun rasu bayan jiragen ruwa biyu na 'yan ci-rani sun kife a gaɓar tekun Libya
DR Congo da M23 sun cim ma yarjejeniyar zaman lafiya 'ta tarihi' a Qatar
AfDB zai ba Nijar CFA biliyan 98.7 domin magance matsalar ruwa ta shekara 70 a Zinder
MDD ta yi gargaɗi kan ƙazancewar yaƙin Sudan, ta yi kira kan barin shigar da kayan agaji
An gabatar da GH¢302bn a matsayin kasafin kuɗin Ghana na 2026 ga majalisar dokokin ƙasar
Sojojin Sudan sun daƙile harin RSF kan filin jirgin sama da dam a arewacin ƙasar
Rubio ya nemi a daina bai wa RSF makamai, ya ɗora wa rundunar laifi kan kashe-kashe a Al Fasher
Dalilin da ya sa TikTok ya goge bidiyoyi miliyan 1.5 da 'yan Uganda suka wallafa
Mutum 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana – Rahotanni
Mahaucin Al Fasher: Yadda hotonsa ya zama alamar bakin cikin Sudan
UN Women: Mata da 'yan mata 11M suna fama da matsanancin ƙarancin abinci a Sudan sakamakon yaƙi