| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
NNPC na tattaunawa da kamfanin China domin farfaɗo da matatun man Nijeriya
Ƙasar da ta fi samar da ɗanyen mai a Afrika tana neman yadda za ta farfado da matatun manta bayan shekaru na asara da rashin aiki yadda ya kamata.
NNPC na tattaunawa da kamfanin China domin farfaɗo da matatun man Nijeriya
Direbobi na jira a layin domin shan mai a wani gidan man NNPC a Abuja. / Reuters
5 Fabrairu 2026

Kamfanin man Nijeriya, NNPC tana tattaunawa da wani kamfanin China game da ɗaya daga cikin matatun man kamfanin ƙasar, kamar yadda shugaban kamfanin man ya bayyana ranar Laraba.

Shugaban kamfanin NNPC Bayo Ojulari ya ce kamfanin na neman masu gudanarwa ƙwararru a matsayin masu zuba jari wajen farfaɗo da matatun man ƙasar guda huɗu bayan shekaru na asara da rashin aiki yadda ya kamata.

Ya ce bincike na cikin gida da aka yi jim kaɗan bayan ya karɓi ragamar kamfanin a watan Afriilun da ya gabata ya nuna cewa matatun man suna tafka asara mai yawa da tsadar kuɗaɗen gudanarwa da kuma kashe kuɗi mai yawa kan ‘yan kwangila yayin da man da ake tacewa ya kasance kaɗan.

Kwamitin gudanarwa na NNPC ya amince da wata dabara ta kawo ƙwararru masu gudanar da matatun mai waɗanda ke da tabbatacciyar ƙwarewa maimakon ‘yan kwangila, in ji Ojulari, yana mai cewa kamfanin na cikin wata tattaunawa da ta yi nisa da wasu da ke son shiga harkar.

"Yanzu haka daga wani zama nake da ɗaya daga cikin waɗanda za su iya zuba jari," in ji Ojulari, ba tare da ba da suna ba.

"Za su ziyarci matatar gobe domin gani da ido. Wani kamfanin China ne da ke da ɗaya daga cikin matatar mai mafi girma a China."

Nijeriya ta shafe shekaru tana fama da ƙoƙarin gyara tsofaffin matatunta wadanda aikinsu ya yi ƙasa da abin da ya kamata su iya yi, lamarin da ya tilasta wa ƙasar da ta fi samar da ɗanyen mai a Afirka ta dogara kan shigar da tacaccen mai.

Gwamnatin na fatan cewa sabuwar alaƙa ta haɗin gwiwa za ta taimaka wajen kawo ƙarshen wannan matsalar.

Ojulari ya ce an dakatar da aiki a matatun domin ba da lokaci na gwada hanyoyin da ake da su na farfaɗo da su, lamarin da ke faruwa a lokacin da aka ƙaddamar da matatar man Dangote, abin da ya ba "dama" ta samar da mai a gida.

Ya ce NNPC ba za ta sayar da matatun man ba, amma za ta sallamar da wani ɓangare na hannayen jarinsu ga abokan hulɗa domin tabbatar da cewa matatun sun iya dogaro da kansu a ayyukansu.

Rumbun Labarai
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya