| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
Za a fara azumin Ramadan na 2026 ranar Laraba a Saudiyya
Sanarwar ta biyo bayan rahotanni daga kwamitocin ganin wata da aka amince da su a fadin Masarautar, bisa ga tsarin Musulunci.
Za a fara azumin Ramadan na 2026 ranar Laraba a Saudiyya
Za a fara azumin Ramadan na 2026 ranar Laraba a Saudiyya / Reuters
17 Fabrairu 2026

Kotun Kolin Saudiyya ta sanar da yammacin ranar Talata cewa an ga jinjirin wata na Ramadan, inda ta tabbatar da cewa a ranar Laraba za a tashi da azumin shekarar 1447 ta hijira waddace ta yi daidai da 2026.

Sanarwar ta biyo bayan rahotanni daga kwamitocin ganin wata da aka amince da su a fadin Masarautar, bisa ga tsarin Musulunci.

Da wannan tabbacin, Musulmai a fadin Saudiyya za su fara azumi a ranar Laraba, inda za su shafe tsawon kwana 29 ko 30 suna azumin.

Ramadan lokaci ne na ibada ta ruhaniya wadda ake yi kullum tsawon watan gaba ɗaya, tun daga fitowar alfijir zuwa faɗuwar rana.

Masallatan Masarautu a faɗin Masarautar suna shirin karɓar masu ibada don yin sallar Taraweeh, yayin da hukumomi suka kammala shirye-shirye don tabbatar da ayyukan ibada cikin sauƙi a cikin watan mai tsarki.

Hukumomin gwamnati da cibiyoyi masu zaman kansu su ma an shirya su aiwatar da lokutan aiki da aka daidaita bisa ga jadawalin watan Ramadan.

Rumbun Labarai
Iran ba za ta amince da bukatu barkatai ba - Shugaba Pezeshkian
Trump ya yi barazanar ɗaukar 'mataki mai tsanani' kan Iran yayin da Netanyahu ya tafi Washington
Fidan na Turkiyya ya ce amfani da hare-haren sama ba zai rushe gwamnatin Iran ba
Shugaban Iran Pezeshkian ya bayyana tattaunawar nukiliya da Amurka a matsayin 'ci gaba' ga Tehran
Turkiyya da Saudiyya sun jaddada goyon bayansu ga haɗin kan Somaliya da zaman lafiyar yankin
Khamenei ya yi gargaɗi kan yaƙin yanki idan Amurka ta kai hari kan Iran
Iran ta ayyana rundunonin sojin ƙasashen Turai a matsayin 'ƙungiyoyin ta'addanci'
A 'shirye' Iran take don 'yarjejeniyar nukiliya ta gaskiya da adalci': Ministan Harkokin Wajen Iran
Waɗanne abubuwa ne za su iya faruwa idan Amurka ta kai hari Iran?
Iran ta ce duk maƙociyar da ta bari aka yi amfani da ita wurin kai mata hari 'abokiyar gaba' ce
Isra'ila na karya yarjejeniyar tsagaita wuta a Lebanon, ta ci gaba da kai hari
Manyan jami'an China sun tattauna da Ƙungiyar OIC a yanayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke ƙara muni
Yaƙin da ake yi da ta'addancin Daesh yana ƙara ƙarfi: Erdogan
Iran ta gargaɗi Amurka: 'Za mu ɗauki kowane irin hari a matsayin cikakken yaƙi a kanmu'
Turkiyya ba ta goyon bayan tsoma bakin ƙasashe waje a kan Iran – Erdogan
Adadin mutanen da suka mutu a zanga-zangar Iran ya kai  4,000: Rahoto
Syria ta cim ma tsagaita wuta don karɓe iko da arewa maso gabas daga hannun ‘yan ta’addan YPG
Iran ta sha alwashin gwabza yaƙi da duk ƙasar da ta yi gangancin kai wa Khamenei hari
Syria ta ayyana harshen Kurdanci a matsayin 'harshen ƙasa', sannan ta ba Kurdawa haƙƙin 'yan ƙasa
An buɗe sararin samaniyar Iran bayan rufe shi na wucin-gadi