| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
1 minti karatu
Za a fara azumin Ramadan na 2026 ranar Laraba a Saudiyya
Sanarwar ta biyo bayan rahotanni daga kwamitocin ganin wata da aka amince da su a fadin Masarautar, bisa ga tsarin Musulunci.
Za a fara azumin Ramadan na 2026 ranar Laraba a Saudiyya
Za a fara azumin Ramadan na 2026 ranar Laraba a Saudiyya / Reuters
17 Fabrairu 2026

Kotun Kolin Saudiyya ta sanar da yammacin ranar Talata cewa an ga jinjirin wata na Ramadan, inda ta tabbatar da cewa a ranar Laraba za a tashi da azumin shekarar 1447 ta hijira waddace ta yi daidai da 2026.

Sanarwar ta biyo bayan rahotanni daga kwamitocin ganin wata da aka amince da su a fadin Masarautar, bisa ga tsarin Musulunci.

Da wannan tabbacin, Musulmai a fadin Saudiyya za su fara azumi a ranar Laraba, inda za su shafe tsawon kwana 29 ko 30 suna azumin.

Ramadan lokaci ne na ibada ta ruhaniya wadda ake yi kullum tsawon watan gaba ɗaya, tun daga fitowar alfijir zuwa faɗuwar rana.

Masallatan Masarautu a faɗin Masarautar suna shirin karɓar masu ibada don yin sallar Taraweeh, yayin da hukumomi suka kammala shirye-shirye don tabbatar da ayyukan ibada cikin sauƙi a cikin watan mai tsarki.

Hukumomin gwamnati da cibiyoyi masu zaman kansu su ma an shirya su aiwatar da lokutan aiki da aka daidaita bisa ga jadawalin watan Ramadan.

Rumbun Labarai
Erdogan na Turkiyya ya yi gargaɗin cewa tashin hankalin Gabas ta Tsakiya ya kai matakin 'ban tsoro'
A shirye Iran take ta yi arangama da dakarun ƙasa na Amurka: babban jami'in diflomasiyya
Ankara na da ‘yancin mayar da martani don kare Turkiyya daga yaƙin Amurka-Isra'ila da Iran
Iran ta ce ta kai wa jirgin ruwan dakon mai na Amurka hari a Gulf
Mafi yawan Amurkawa ba sa goyon bayan yaƙin Amurka kan Iran: Ƙuri'ar jin ra'ayi
Iran ta yi iƙirarin kashe sojojin Amurka 500 a cikin kwanaki biyar na yaƙi
Shin yaƙin Amurka da Isra’ila a Iran duk dabara ce ta sake mamayar yankin Gabas ta Tsakiya?
'An gaya wa dakarun Amurka cewa yaƙin Iran ‘ƙudirar Ubangiji’ ce don kawo ƙarshen duniya'
Amurka ta yi asarar kayayyakin sojin na kusan $2bn a kwanaki 4 na yaƙi da Iran
Iran ta ce babu zancen tattaunawa da Amurka, ta sha alwashin kare kanta kawai
Ministan Turkiyya Fidan na yin tuntubar diflomasiyya a tsaka da hare-haren Amurka da Isra’ila a Iran
Yaƙin Iran da Isra'ila ya sa tafiya Umara zuwa Saudiyya na fuskantar barazana
Iran ta ce ta kai hari a wurare aƙalla 500 na Isra'ila da Amurka
Ƙasashen Afirka sun yunƙura don kare jama'arsu da ke  Gabas ta Tsakiya
Me ya rage wa Iran bayan Khamenei?
Jiragen yaƙin Amurka da dama sun faɗi a Kuwait, in ji ma'aikatar tsaron Kuwait
Iran ta harba makamai masu linzami Isra'ila, 9 sun mutu a Beit Shemesh, 12 sun mutu a faɗin ƙasar
Iran ta kafa majalisar jagorancin wucin-gadi a Iran bayan kashe Khamenei
Nijeriya, Senegal da Libya sun buƙaci a tsagaita wuta yayin da Isra'ila-Amurka ke rikici da Iran
Iraniyawa suna zanga-zanga bayan Amurka da Isra'ila sun kashe Khamenei