Shugaban Nijar ya naɗa sabon shugaban hafsan sojojin ƙasar, kamar yadda gidan talabijin na ƙasa ya ruwaito a ranar Jumma’a, bayan yunƙurin tawaye da wasu sojoji suka yi a watan da ya gabata, wanda ya girgiza ikonsa.
Sojojin da ba su gamsu da halin da ake ciki ba sun kai hari kan wasu muhimman wurare a Yamai, tare da fakewa a wani muhimmin sansanin soji da ke filin jirgin sama yayin yunƙurin tawayen.
“Ta hanyar wata doka da Janar Abdourahamane Tiani ya sanya wa hannu a ranar 11 ga Satumba, 2026, ya naɗa Birgediya Janar Mamane Sani Kiaou a matsayin shugaban hafsan rundunar sojojin ƙasar,” kamar yadda gidan talabijin na ƙasar ya ruwaito a cikin wata sanarwa.
Kiaou, wanda a baya ya riƙe matsayin shugaban hafsan sojojin ƙasa, zai maye gurbin Janar Moussa Salaou Barmou.
Sanarwar ba ta bayyana dalilin da ya sa aka sauke Barmou daga muƙaminsa ba.
Sanarwar ta ƙara da cewa Tiani ya kuma naɗa Janar Abdourahmane Abou Zataka domin maye gurbin Kiaou a matsayin shugaban hafsan sojojin ƙasa.
Abokan aikinsa sun bayyana Kiaou a matsayin “ƙwararren kwamandan yaƙi”, inda ya jagoranci yaƙi da ƙungiyoyin ’yanta’adda a yankin Tillaberi da ke yammacin Nijar da kuma yankin Diffa da ke kudu maso gabashin ƙasar.
Kafofin yaɗa labaran Nijar sun ruwaito cewa kwanan nan ya kammala rangadin muhimman sansanonin soji na ƙasar, wanda aka shirya domin “dawo da haɗin kai tsakanin sojoji.”
Kiaou ya kuma jagoranci tattaunawar da ta haifar da janye dakarun Faransa da Amurka daga Nijar bayan sauyin gwamnati a shekarar 2023.
Tiani ya ƙara yauƙaƙa alaƙarsa da ƙasar da Rasha, tare da nisanta ta daga ƙasashen Yamma, musamman Faransa, wadda ta kasance tsohuwar ƙasar da ta yi wa Nijar mulkin mallaka.
Gidan talabijin na ƙasar ya ruwaito shugaban Nijar ɗin a wancan makon yana zargin Faransa da a yunƙurin tawayen da aka yi a watan da ya gabata, zargin da Faransar ta musanta.


















