Matatar Mai ta Dangote da ke Nijeriya ta sanar da shirin fara sayar da hannayen jarinta a karon farko a cikin watan Satumba.
“Burinmu shi ne mu tabbatar da mun ninka ƙarfin matatar man...abin da zai kai mu ga tace ganga miliyan 1.4 a kowace rana. A cikin kwanaki 10 zuwa 12 masu zuwa za a fara sayar da hannayen jarin a karon farko," in ji Aliko Dangote ga masu zuba jari da masu sharhi a Botswana, yayin da yake ziyartar ƙasar ta ke Kudancin Afirka.
Ana sa ran matatar, mallakar mutumin da ya fi kowa kuɗi a Afirka, za ta nemi tara kusan dala biliyan 5 a cikin abin da zai iya zama babban hannun jari a karon farko a nahiyar.
Dangote bai bayyana ribar matatar man ba, amma masana'antar ta amfana da riba mai yawa yayin da rikice-rikice a Gabas ta Tsakiya suka ƙara buƙatar samar da wasu hanyoyin na daban don samun man fetur.
Matatar mai iya tace gangar danyen mai 650,000 a kowace rana ta kai matakin yin cikakken aiki a watan Fabrairu kuma ta riga ta gwada fitar da ganga 700,000 a kowace rana.
Ɗan kasuwar ya kuma ce jerin kamfanonin Siminti na Dangote (DANGCEM.LG), wanda zai buɗe sabon shafi, wani kamfani mai tasowa a daularsa ta masana'antu, a kasuwar hannayen jari ta London, zai iya shiga kasuwar a watan Oktoba, kuma hakan wani mataki ne da zai iya faɗaɗa damarsa ga masu zuba jari na ƙasashen waje.
Dangote kuma yana shirin gina sabuwar matatar mai a gabar tekun Kenya tare da haɗin gwiwar gwamnatocin Gabashin Afirka. Aikin, wanda ake sa ran zai ɗauki shekaru uku kafin a kammala, zai samar da albarkatun mai da aka tace ga Kenya da ƙasashen da ke makwabtaka, wanda zai taimaka wajen rage dogaron Gabashin Afirka kan man fetur da ake shigowa da shi daga ƙasashen waje.
Hakan zai samar da babban zuba jarin matatar mai ta Dangote a wajen Najeriya. "Za mu ƙaddamar da aikin a ranar 30 ga Satumba," in ji shi.






















