| Hausa
TATTALIN ARZIKI
2 minti karatu
Matatar Dangote ta Nijeriya za ta fara sayar da hannayen jari a karon farko nan da ‘yan kwanaki
Nan da kwanaki 10 zuwa 12 a karon farko, za a fara sayar da hannayen jarin Matatar Mai ta Dangote, matata mafi girma a nahiyar, in ji mamallakinta, Aliko Dangote, a ranar Alhamis.
Matatar Dangote ta Nijeriya za ta fara sayar da hannayen jari a karon farko nan da ‘yan kwanaki
Hayaki na tashi daga bututu a matatar mai ta Dangote da ke Lekki, Lagos a ranar 2 ga Maris 2026. REUTERS

Matatar Mai ta Dangote da ke Nijeriya ta sanar da shirin fara sayar da hannayen jarinta a karon farko a cikin watan Satumba.

“Burinmu shi ne mu tabbatar da mun ninka ƙarfin matatar man...abin da zai kai mu ga tace ganga miliyan 1.4 a kowace rana. A cikin kwanaki 10 zuwa 12 masu zuwa za a fara sayar da hannayen jarin a karon farko," in ji Aliko Dangote ga masu zuba jari da masu sharhi a Botswana, yayin da yake ziyartar ƙasar ta ke Kudancin Afirka.

Ana sa ran matatar, mallakar mutumin da ya fi kowa kuɗi a Afirka, za ta nemi tara kusan dala biliyan 5 a cikin abin da zai iya zama babban hannun jari a karon farko a nahiyar.

Dangote bai bayyana ribar matatar man ba, amma masana'antar ta amfana da riba mai yawa yayin da rikice-rikice a Gabas ta Tsakiya suka ƙara buƙatar samar da wasu hanyoyin na daban don samun man fetur.

Matatar mai iya tace gangar danyen mai 650,000 a kowace rana ta kai matakin yin cikakken aiki a watan Fabrairu kuma ta riga ta gwada fitar da ganga 700,000 a kowace rana.

Ɗan kasuwar ya kuma ce jerin kamfanonin Siminti na Dangote (DANGCEM.LG), wanda zai buɗe sabon shafi, wani kamfani mai tasowa a daularsa ta masana'antu, a kasuwar hannayen jari ta London, zai iya shiga kasuwar a watan Oktoba, kuma hakan wani mataki ne da zai iya faɗaɗa damarsa ga masu zuba jari na ƙasashen waje.

Dangote kuma yana shirin gina sabuwar matatar mai a gabar tekun Kenya tare da haɗin gwiwar gwamnatocin Gabashin Afirka. Aikin, wanda ake sa ran zai ɗauki shekaru uku kafin a kammala, zai samar da albarkatun mai da aka tace ga Kenya da ƙasashen da ke makwabtaka, wanda zai taimaka wajen rage dogaron Gabashin Afirka kan man fetur da ake shigowa da shi daga ƙasashen waje.

Hakan zai samar da babban zuba jarin matatar mai ta Dangote a wajen Najeriya. "Za mu ƙaddamar da aikin a ranar 30 ga Satumba," in ji shi.

Rumbun Labarai
Kuɗin Ghana ya koma fuskantar matsi, na Uganda na farfaɗowa, na Nijeriya zai iya sauyawa kaɗan
Amurka ta yi barazanar saka wa tattalin arzikin Iran takunkumin da 'duniya ba ta taɓa gani ba'
Gwamnatin Nijeriya za ta farfado da burtalan kiwo 417 a faɗin ƙasar
Za a gyara kamfanin NNPC tare da sayar da hannayen jarinsa a kasuwar hannayen jarin Nijeriya —Tinubu
Matatar Dangote ta fitar da tan fiye da 400,000 na man jiragen sama zuwa Turai a watan Yuli - Rahoto
Hukumar Kasuwanci Marar Shinge ta Afirka ta sanya hannu da wani kamfanin Nijeriya don inganta fito
A lokacin da cututtuka suka tsallaka iyaka: Manoman Afirka na neman sabbin matakan kariya
Farashin fetur a Amurka ya tashi sakamakon tsaiko a Hormuz da sanarwar Houthi ta rufe Bahar Maliya
ECOWAS ta sanya hannu kan yarjejeniyar tallafa wa aikin bututun iskar gas na Nijeriya da Morocco
Ƙungiyar EU ta sanar da sanya sabbin takunkumai kan cinikayyar zinare a Sudan
Hauhawar farashin kayayyaki a Ghana ta ƙaru a wata uku a jere da 5.3% a Yunin 2026
Wa yake amfana a lokacin da tattalin arzikin duniya ke ci da wuta sakamakon yaƙi?
Abubuwan da dalar Amurka Tiriliyan 1.1 mallakin Elon Musk za ta iya yi a Afirka
Elon Musk ya zama tiriloniya na farko a tarihin duniya
An zargi matatar mai mafi girma a Afirka da ƙoƙarin yin babakere game da man Nijeriya
Biliyoyin kudi da gangunan mai: Yadda matatar mai ta Dangote ke ƙarfafar Afirka da makamashi
China ta faɗaɗa janye haraji baki ɗaya ga kayan da ta shigar daga ƙasashen Afirka 53
Wasu daga waje na ƙoƙarin daƙile ci-gaban Afirka, in ji  Dangote
Ghana ta bai wa wani kamfanin ƙasar lasisin haƙar zinare kan $1bn
Shigar kuɗaɗe daga waje cikin Nijeriya don zuba jari ta ƙaru da kusan kashi 90% a 2025 – Hukumomi