| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Trump ya yi gargaɗin cewa Amurka za 'hallaka da lalata' Iran idan Tehran ta kai masa hari
"An riga an ba da umarni, kuma rundunar sojin Amurka tana a shirye, kuma tana da niyya da iko, na tsawon shekara ɗaya, wanda za a iya tsawaitawa, ta hallaka da kuma lalata gaba ɗaya dukkan ƙasar Iran," a cewar Trump.
Trump ya yi gargaɗin cewa Amurka za 'hallaka da lalata' Iran idan Tehran ta kai masa hari
Kalaman na Trump, waɗanda ya yi a kan shafin sada zumuntansa na Truth Social, za su iya sake tayar da hankula a a Gabas Ta Tsakiya

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce ya ba da umarni ga rundunar sojin ƙasar ta shirya domin ƙaddamar da hare-haren kan Iran idan gwamnatin Tehran ta yi ƙoƙarin kashe ni.

"An ɗana makamai masu linzami 1000 inda suke kallon Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma ƙarin dubbai za su iya biyo baya nan-take idan gwamnatin Iran ta aiwatar da barazanarta, wadda ta furta a sassan duniya da yawa, ta kashe ko kuma ta yi ƙoƙarin kashe shugaban Amurka mai mulki, a wannan karon, NI!," kamar yadda ya bayyana a wani saƙo a shafin Truth Social.

"An riga an ba da umarni, kuma rundunar sojin Amurka tana shirye, kuma tana da niyya da iko na tsawon shekara ɗaya, wanda za a iya tsawaitawa, ta hallaka da kuma lalata dukkan ƙasar Iran."

Masu AlakaTRT Afrika - Yarjejeniyar fahimtar juna tasakanin Amurka da Iran ta 'kammala' bayan sa hannun Trump da Pezeshkian

Kalaman na Trump za su iya sake tayar da hankali a Gabas ta Tsakiya.

An kwashe kwanaki Amurka tana kai hare-haren a Iran yayin da Iran take mayar da martani tare da hare-hare kan kayayyakin Iran a faɗin Gabas ta Tsakiya.

Tun da farko Trump ya ayyana cewa yarjejeniyar tsagaita wuta da Iran ta "rushe," amma Washington ta yarda ta ci gaba da tattaunawar da Tehran ta nemi a yi.

Kwanan baya Isra’ila ta ba da “bayanan sirri” ga Amurka da ke nuna cewa Iran ta kitsa wani sabon shiri na kashe Trump, in ji wani rahoto na jaridar Wall Street Journal.​​​​​​​