Shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta Turkiyya ya yi gargaɗi kan rikicin Iran na iya zama na duniya

Rikicin da ake yi a Iran a halin yanzu na ta "saurin rikidewa zuwa wani rikicin duniya, kuma akwai barazanar ya zama wani rikicin da zai shafi mutane biliyan takwas," in ji Ibrahim Kalin.

By
Ya ce yaƙin Rasha da Ukraine da ya fara a 2022 kwanan nan ya shiga shekara ta biyar, kuma har yanzu babu tabbataccen bayani kan yadda zai ƙare. / AA

Shugaban Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa ta Turkiyya ya yi gargaɗi cewa yaƙin da ke gudana tsakanin Isra'ila, Amurka, da Iran na iya ƙaruwa ya zama rikici mai fadi a duniya idan ya ci gaba.

Yayin da yake magana a Taron STRATCOM na 2026 a Istanbul a ranar Asabar, Ibrahim Kalin ya ce: "Tun daga annobar Corona, duniyarmu tana jerin ƙalubale, rikice-rikice, da ruguje-ruguje."

Ya ce yaƙin Rasha da Ukraine da ya fara a 2022 kwanan nan ya shiga shekara ta biyar, kuma har yanzu babu tabbataccen bayani kan yadda zai ƙare.

Kalin ya ce kuma har yanzu ana jin illolin yakin kisan ƙare-dangi na Isra'ila a Gaza da ya fara a 7 ga Oktoban 2023.

"Yayinda ƙoƙarin samar da zaman lafiya a Gaza ke ci gaba, take-taken Isra'ila da manufofinta na mulkin mallaka da mamaya suna ci gaba ba tare da dakatarwa ba," in ji shi.

Kan abubuwan da ke faruwa a yankin, Kalin ya ce yaƙin kwanaki 12 tsakanin Isra'ila da Iran a watan Yuni da ya gabata ya zama zakaran gwajin dafi kan yaƙin Iran na yanzu.

"A halin yanzu muna tsakiyar yaƙin Isra'ila da Amurka kan Iran da ya fara a 28 ga Fabrairu kuma ya ci gaba na kusan wata guda," in ji shi.

Kalin ya ce Turkiyya ta yi ƙoƙarin diflomasiyya sosai don hana ɓarkewar yaƙin Iran da hana yaɗuwarsa, yana gargaɗi cewa akwai haɗarin ya bazu fiye da yankin.

"Abin baƙin ciki, yaƙin yankin da Isra'ila ta fara na tafiya cikin sauri zuwa zama rikicin duniya," kamar yadda shugaban ƙasar ya yi gargaɗi, in ji shi. Yana iya zama "yaƙi da mutane biliyan takwas za su biya farashin sa."

"Dukkan ƙoƙarinmu shi ne, farko-farko, a sa wannan yaƙin ya ƙare cikin gaggawa," in ji shi.

Turkiyya ba ta taɓa hura wutar rikici ba

Ya kuma gargaɗe cewa rikicin zai iya zurfafa rarrabuwar kawuna a yankin.

Kalin ya jaddada cewa Turkiyya ba za ta yi wani abu don ƙara tsananin rarrabuwar ba.

"Turkiyya ba ta kasance ba kuma ba za ta kasance ɓangare mai hura wutar rikici ba," in ji shi. "Idan ya zama dole, za mu riƙe garwashin wuta da hannunmu mu domin ya huce a kan kirjinmu, amma ba za mu taɓa jefa ta cikin wutar rikici ba."

Ya ce yaƙin da ake yi wa Iran ba shi da tushe a doka a ƙarƙashin dokar ƙasa da ƙasa.

Kalin ya kuma yi gargaɗi game da ƙoƙarin ƙirƙirar sabbin abubuwan da aka riga aka kammala a fili a yankin.

"Mun sani sosai cewa waɗanda suka fara wannan yaƙin na ƙoƙarin ƙirƙirar sabbin abubuwa a Lebanon, Syria, yankunan Falasdinu, da wasu wurare — ta hanyar manufofin hallakawa, mamaya da mulkin mallaka," in ji shi.

Ya ƙara da cewa Turkiyya ba za ta yarda a yi watsi da hakkokin Falasdinawa ba.

"Ba za mu yarda a kwace muhimman hakkokin Falasdinawa ta hanyar abubuwan da aka riga aka kammala ba, ko a yi watsi da take-taken haƙƙin bil’adama da ake yi a Gaza da Yammacin Kogin Jordan,” in ji shi.

"Harin Iran kan ƙasashen Gulf ba abin yarda ba ne," in ji Kalin. "Amma dole ne mu ƙara tuna wanda ya fara yaƙin."

Ya ce Turkiyya na goyon bayan ƙoƙarin diflomasiyya na tattaunawa, ciki har da ƙoƙarin da Pakistan ta yi.

"Muna da cikakken goyon bayan hannun taimako na 'yan'uwa Pakistan da suka miƙa a wannan al'amari," in ji shi.

Duk da haka, Kalin ya ce Isra'ila ta raunana ƙoƙarin buɗe hanyar tattaunawa.

"Kamar kafin yaƙin, muna ganin cewa Isra'ila tana yin ƙoƙari sosai don yin zagon ƙasa a yunƙurin sulhu da hanyoyin tattaunawa," in ji shi.

Tashin hankali a Gabas Ta Tsakiya ya ƙaru tun 28 ga Fabrairu, lokacin da Amurka da Isra'ila suka kaddamar da wani hari na haɗin gwiwa kan Iran wanda zuwa yanzu ya kashe fiye da mutane 1,340, ciki har da wanda Jagoran Addini na ƙasar Ali Khamenei.

Iran ta mayar da martani da harin jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami, inda take kai hari kan Isra'ila da ƙasashen Gulf da ke masaukin kadarorin soja na Amurka.

‘Sadarwa ƙoƙari ne na gina ma'ana’

Baya ga wannan rikicin, Kalin ya kuma gargaɗi cewa wannan zamanin a duniya ya cika da bayanai amma tana rabuwa da gaskiya.

"Muna rayuwa a wani zamani inda bayanai suka yalwata, ilimi ke raguwa, kuma hikima kusan ta ɓace," in ji shi.

"Sadarwa ba kawai ƙoƙari ba ne na isar da bayanai da saƙonni," in ji shi. "Sadarwa kuma ƙoƙari ne na gina ma'ana."

"Idan ba ka ba wani suna ba, ba naka ba ne. Idan ba ka ba labari ba, ba labarinka ba ne," in ji Kalin, yana kira ga al'ummomi su haɓaka nasu tsarin tunani da labarai.