Zaben Nijeriya na 2027: Matakan Tinubu na rage talauci da alƙawarin Atiku na mayar da tallafin fetur
NIJERIYA
7 minti karatu
Zaben Nijeriya na 2027: Matakan Tinubu na rage talauci da alƙawarin Atiku na mayar da tallafin feturBayan shekaru uku da aka cire kudin gaso-gaso a Najeriya, jayayyar dawo da shi ta koma cikin tattaunawa a kan siyasa a lokacin da kasar take zuwa zaben 2027.
Tallafin man fetur na ƙara zama babban batun yaƙin neman zaɓe gabannin zaɓen 2027 na Nijeriya / TRT Afrika

Alkawarin da dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar adawa ta African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya yi na dawo da tallafin man fetur idan aka zaɓe shi, ya sake farfaɗo da gasar neman kujerar da ke Aso Rock, wato cibiyar mulkin Nijeriya.

Haka kuma, alkawarin ya sake mayar da batun tallafin man fetur a tsakiyar muhawarar jama’a a Nijeriya, ƙasar da ta fi kowace ƙasa yawan al’umma a Afirka.

A cikin wasu hirarrakin da ya yi da kafafen yaɗa labarai a baya-bayan nan, Atiku, wanda ya taɓa zama mataimakin shugaban ƙasa a ƙarƙashin tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo, ya soki matakin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ɗauka na cire tallafin ba zato ba tsammani, yana mai zargin cewa matakin ya ƙara tsananta wahalhalun tattalin arziki da ’yan Nijeriya da dama ke fuskanta.

Atiku yana matsayin mataimakin shugaban ƙasa a lokacin da gwamnatin Obasanjo ta fara rage tallafin man fetur a hankali.

Yanzu ya ce ba ya buƙatar masana su bayyana masa illar cire tallafin. Ya ce yana ganin hakan ne ta hanyar ƙaruwar tsadar rayuwa da miliyoyin ’yan Nijeriya ke fuskanta.

Alkawarin nasa ya samu karɓuwa sosai a kafafen intanet, inda ’yan Nijeriya da dama suka bayyana goyon bayansu ga matsayinsa tare da danganta cire tallafin da hauhawar farashin sufuri da kayan abinci.

Batun ya kuma sa Shugaba Tinubu da gwamnonin jihohin Nijeriya 36 suka sanar da matakan da za su rage kuɗin sufuri daga ranar 1 ga Oktoban 2026.

Tunawa da 'Occupy Nigeria'

Nijeriya ta fara rage tallafin man fetur a hankali tun kafin shekarar 2012. Sai dai batun ya kai wani mataki mai tsanani a ranar 1 ga Janairun 2012, lokacin da Shugaban ƙasa na wancan lokacin, Goodluck Jonathan, ya sanar da cire tallafin.

Matakin ya haifar da zanga-zanga a faɗin Nijeriya da kuma wasu ƙasashen ƙetare.

Zanga-zangar, wadda aka fi sani da Occupy Nigeria, ta zama ɗaya daga cikin manyan zanga-zangar da aka taɓa gudanarwa a tarihin baya-bayan nan na ƙasar.

Cire tallafin ya sa farashin litar man fetur ya tashi daga naira 65 zuwa naira 141 — farashin da ake sayar da man a wasu ƙasashen maƙwabta da suka haɗa da Nijar, Kamaru, Benin da Chadi.

Ga ’yan Najeriya da dama, ƙarin farashin ya yi yawa matuƙa.

Sun fito kan tituna domin nuna adawa da abin da suke gani a matsayin cire ɗaya daga cikin ƴan fa’idojin da suke samu a matsayinsu na ’yan ƙasar da ke samar da man fetur.

Sai dai gwamnati ta yi iƙirarin cewa ba za a iya ci gaba da biyan tallafin ba.

A cewar tsohon gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Sanusi Lamido Sanusi, wanda yanzu shi ne Sarkin Kano, Nijeriya ta kashe dala biliyan 8 wajen tallafin man fetur a shekarar da ta gabata.

Da yake jawabi a wani taron masu ruwa da tsaki da Ƙungiyar Mamallaka Jaridun Nijeriya ta shirya a watan Disambar 2011, Sanusi ya ce ƙasar ta kashe naira tiriliyan 1.4 — wato kashi ɗaya bisa uku na jimillar kuɗin da gwamnati ta kashe — wajen tallafa wa kayayyakin man fetur.

Ya ce ya kamata Nijeriya ta fi mayar da tallafi ne kan samar da man fetur maimakon amfani da shi.

Sanusi ya yi gargadin cewa ci gaba da tallafin zai bar gwamnatocin da za su zo nan gaba da nauyin bashi wanda ba za a iya ɗauka ba.

Sai dai ’yan Nijeriya da dama sun yi watsi da hujjar gwamnati, kuma zanga-zangar ta ci gaba.

Ƙungiyar Ƙwadago ta Nijeriya (NLC) ta shiga zanga-zangar, sannan a ranar 5 ga Janairu ta ba gwamnati wa’adin rufe ƙasar baki ɗaya matuƙar ba ta janye matakin da ta ɗauka ba.

Abin da ya fara a matsayin zanga-zanga ba tare da wani shiri na musamman ba, yanzu ya samu shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago da gwamnati za ta iya tattaunawa da su.

Bayan tattaunawa da ƙungiyoyin ƙwadago, an dakatar da barazanar gudanar da yajin aikin gama-gari a faɗin ƙasar.

A ƙarshe, wasu ’yan Nijeriya sun rasa rayukansu yayin zanga-zangar, sannan gwamnati ta ɗan janye matakin cire tallafin tare da ƙaddamar da Shirin SURE-P, wato Shirin Sake Zuba Jari da Ƙarfafa ’Yan Ƙasa.

Abin da ke ƙara ƙarfafa fasa-ƙwauri

Muhawarar tallafin man fetur ba ta gushe ba bayan Goodluck Jonathan ya bar mulki a shekarar 2015, Muhammadu Buhari kuma ya zama shugaban ƙasa.

A wa’adin mulkin Buhari na biyu, gwamnati ta ƙara bayyana aniyarta ta kawo ƙarshen tallafin man fetur.

A watan Janairun 2022, ministar kuɗin Nijeriya a lokacin, Zainab Ahmed, ta ce gwamnatin tarayya na nan daram kan aniyarta ta cire tallafin.

Daga ƙarshe dai gwamnatin Buhari ba ta aiwatar da cikakken cire tallafin ba.

Sai dai Tinubu, wanda a lokacin yake yaƙin neman zaɓen maye gurbin Buhari, ya riga ya gargaɗi ’yan Nijeriya cewa zai cire tallafin.

“Wannan shi ne gaskiya. Sai dai idan ba ku sani ba... kuma ni ne zan lashe wannan zaɓe,” kamar yadda ya ƙara da cewa.

Tinubu yana magana ne kan fasa-ƙwaurin man fetur daga Nijeriya zuwa ƙasashen maƙwabta, inda ake iya sayar da shi a farashi mafi tsada.

Bambancin farashin ya ƙarfafa masu safarar man fetur ta ɓarauniyar hanya su sayi man da ake tallafa wa a Nijeriya sannan su sayar da shi a ƙetaren iyaka domin samun riba.

Masu goyon bayan cire tallafin sun daɗe suna amfani da wannan hujjar bambancin farashi wajen mayar da martani ga kiraye-kirayen cewa Nijeriya ta ci gaba da bayar da tallafin man fetur ga ’yan ƙasarta, kamar yadda wasu manyan ƙasashen da ke samar da man fetur ke yi.

Sanusi ya gabatar da irin wannan hujja a lokacin da yake gwamnan Babban Bankin Nijeriya, inda ya ce bambancin farashin ya sa da wahala a dakatar da safarar man fetur ta ɓarauniyar hanya.

“Me ya sa a Saudiya, inda ake tallafa wa man fetur, ba ku ga irin wannan safara ta barauniyar hanya ba?” kamar yadda ya tambayi masu ruwa da tsaki a watan Disambar 2011.

Ya ce saboda ƙasashen maƙwabta ma suna tallafa wa man fetur, babu wata dama mai yawa ta samun riba ta hanyar ɗaukar man fetur mai tallafi zuwa ƙetaren iyaka.

Sai dai a Nijeriya, ya ce akasin haka ne: man fetur mai tallafi ya fi rahusa sosai idan aka kwatanta da farashinsa a ƙasashen maƙwabta, abin da ya samar da kasuwa mai matuƙar riba ga masu safarar man ta barauniyar hanya.

Alƙawari da aka cika

Tinubu ya lashe zaɓen — kuma ya cika alƙawarin.

A ranar da aka rantsar da shi a watan Mayu 2023, ya sanar da cire tallafin mai da kuma barin naira ta yi gogayya a kasuwar duniya.

Wadannan manufofi biyun suka biyo baya da ƙaruwa mai tsanani a hauhawar farashi da kuma tashin farashin fetur daga kimanin naira 234 zuwa har naira 1,200 a lita ɗaya.

Hauhawar farashin fetur ta sanya farashin sufuri da abinci tashi, wanda ya sa rayuwa ta yi wuya ga iyalai da dama a Nijeriya, in ji Atiku.

Wannan shi ne yanayin da ya biyo bayan alƙawarin sa na mayar da tallafin idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa.

''Ina so in maimaita a fili cewa abin da na faɗa — zan mayar da tallafi, zan mayar,'' in ji Atiku.

''Nijeriya tana da isasshen arziki don kula da jin daɗin 'yan ƙasarta,'' kamar yadda ya ƙara da cewa.

Ya kuma kare matsayinsa bayan ɗaya daga cikin masu magana da yawunsa ya fito ya yi magana mai cin karo da juna kan wannan matsaya, yana cewa cire tallafin ya sa ƙarin 'yan Nijeriya cikin talauci fiye da kowane lokaci a tarihin ƙasar.

Yayin da wasu 'yan siyasa na hamayya ke neman amfani da sha'awar jama'a da matsayar Atiku ta haifar, batun tallafin mai ya sake bayyana a matsayin wata rarrabuwar siyasa.

Batun na iya zama jigon zaɓen shugaban ƙasa na 2027 a Nijeriya — kuma wani gwaji ga sabon yunƙurin Atiku na neman shugabanci.

Yayin da zaɓen Janairu na 2027 ke ƙaratowa, tambayar ita ce ko 'yan Nijeriya za su amince da Atiku kan mayar da tallafin ko kuma za su karɓi matakan sauƙin rayuwa da Tinubu ya ɗauka don rage raɗaɗin cire tallafin.