| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Matar shugaban Nijeriya ta ce akwai buƙatar Nijeriya ta ƙarfafa haɗin gwiwarta da masarautar Saudiyya don gyara tsarin ilimin Almajiri ta hanyar hada karatun Musulunci da na zamani.
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin Almajirai da yaran ba sa zuwa makaranta a Nijeriya

Matar shugaban Nijeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kira ga Saudiyya da ta tallafa wajen faɗaɗa damar samun ilimin zamani ga almajirai da waɗanda ba sa zuwa makaranta, tana mai cewa matakin zai iya taimakawa wajen magance rashin tsaro da kuma inganta makomar ƙasar.

Da take magana a lokacin da ta karɓi baƙuncin Jakadan Saudiyya a Nijeriya, Yousef Mohammed Al-Balawi, a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja ranar Alhamis, Oluremi ta ce akwai buƙatar Nijeriya ta ƙarfafa haɗin gwiwa da Masarautar Saudiyya don gyara tsarin ilimin almajirai ta hanyar haɗa karatun Musulunci da na zamani.

Ta ce wannan tsari zai samar wa yara marasa galihu, musamman waɗanda ke yankin arewacin Nijeriya, ingantattun damarmaki na ilimi tare da bin tsarin koyarwar addinin Musulunci.

"Ina aiki da mata da yara marasa galihu, amma ina matuƙar tausaya wa yara almajirai a arewacin Najeriya. Sun cancanci samun kulawa mafi kyau," in ji matar shugaban ƙasar.

Ta yi gargaɗin cewa rashin magance buƙatun almajirai da yaran da ba sa zuwa makaranta zai iya ta'azzara ƙalubalen tsaro a Nijeriya.

"Idan muka iya samar musu ilimin zamani da na addini, za a samu tsaro a makomar Nijeriya," in ji ta

Kazalika Oluremi ta yi jinjina bisa daɗaɗɗiyar dangantakar diflomasiyya tsakanin Nijeriya da Saudiyya, sannan ta bayyana fatan samun haɗin gwiwa mai zurfi a fannin ilimi da sauran fannoni.

A nasa ɓangaren, jakadan Saudiyya Al-Balawi ya ce ya samu ƙwarin gwiwa daga kyakkyawar tarbar da ya samu tun lokacin da ya isa Nijeriya watanni biyar da suka gabata.

Ya ce tattaunawa da yi da jami'an gwamnatin Nijeriya sun ƙara ƙarfafa dangantaka da ke tsakanin ƙasashen biyu, haka kuma ya nuna ƙwarin gwiwar ci gaba da faɗaɗa haɗin gwiwa.

"Dangatakar ƙasashenmu tana da tarihi mai tsawo, musamman ta fannin addini da al'adu, da kuma yiwuwar zurfafa haɗin gwiwarmu," in ji jakadan yana mai ƙari da cewa a “ƙasashen biyu suna da burin ƙarfafa tattalin arzikinsu.”

Al-Balawi ya samu rakiyar shugaban ma’aikatan ofishin jakadancin Saudiyya a Nijeriya, Mohammed Bukar.

Rumbun Labarai
Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya ta kama wasu mutane da kudade da ake zargin kuɗin fansa ne
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum biyu kan zargin kashe Danshagamu a Kano
Nijeriya ta naɗa sabon kwamandan yaƙi da ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram
NEMA ta karɓi ’yan Nijeriya 180 da aka mayar da su gida daga Libya
Sojojin Nijeriya sun kama wasu da ake zargin masu kai wa ’yanta’adda kayayyaki ne a Jihar Yobe
FIFA ta tura tawaga zuwa Nijeriya don gano ko gwamnati ta tsoma baki a murabus ɗin shugabannin NFF
INEC za ta ƙaddamar da na’urar bibiyar shirye-shiryen zaɓe kai-tsaye
An  kashe mutum 12, an jikkata 2 a sabon harin da Boko Haram ta kai wani ƙauye a Adamawa ta Nijeriya
‘Yanbindiga sun kashe mutum 10, sun sace 40 a wani ƙauyen Sokoto
Gwamnatin Jihar Filato a Nijeriya ta rufe makarantu saboda ɓarkewar cutar mashaƙo
NDC ta yi watsi da jita-jitar da ake yaɗawa kan ba ta da ’yan takarar gwamna a jihohin Nijeriya 12
Sojojin Nijeriya sun ceto mutum 36 da aka sace a kasar, sun kuma halaka ’yanta’adda da dama
‘Yanbindiga sun kashe mutum biyar tare da jikkata uku a wasu ƙauyukan Sokoto
Shari'ar Tinubu a Amurka ta neman haƙƙi ce ba ta laifi ba ce— Fadar Shugaban ƙasa
Darakta Janar na DSS ya umarci jami'ansu da kar su kama kowa yayin da farar-hula suka samu sabani
Nijeriya ta musanta zargin goyon bayan yunƙurin 'juyin mulki' a Nijar
Hukumar DSS ta Nijeriya ta ƙwato bindigogi 676 da harsasai 332,000
INEC za ta yi zaɓen gwaji na Shugaban Ƙasa gabannin zaɓen 2027 na Nijeriya
Ɓarayin daji sun ƙaƙaba harajin naira miliyan 40 kan mazauna wani gari a Sokoto
An lalata makarantu fiye da 1000, an kashe malamai 2,295 a Arewa maso Gabashin Nijeriya - Hukumomi