| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Rundunar Sojin Nijeriya ta ƙaryata wani rahoto na zargin mutuwar kurtu a Depot na Zaria
Rundunar Sojin Nijeriya ta karyata rahoton cewa Ibrahim Nazifi ya mutu yayin horaswa a Depot Zariya, tana mai cewa bai taɓa halartar horaswar ba.
Rundunar Sojin Nijeriya ta ƙaryata wani rahoto na zargin mutuwar kurtu a Depot na Zaria
Rundunar sojin ta yi gargaɗi ga jama’a da su guji yaɗa bayanan da ba a tantance ba / Nigerian army
24 Janairu 2026

Rundunar Sojin Nijeriya ta ƙaryata rahotannin kafafen yaɗa labarai da ke cewa wani ɗan asalin Jihar Gombe mai suna Ibrahim Nazifi ya rasu yayin atisayen horaswa a sansanin horas da kuratan sojoji na Depot da ke Zariya, inda ta bayyana rahotannin a matsayin ƙarya da ruɗani.

A cikin wata sanarwa da Depot ɗin ta fitar ta bayyana cewa bayanan da suke da su sun nuna cewa Nazifi, mai lambar neman shiga aiki 90RRI-GO-9017726, ya yi nasarar tsallake tantancewar ɗaukar soji wadda aka gudanar a watan Disamban 2025, sannan aka zaɓe shi don halartar horaswa a Depot ɗin Zariya. Sai dai rundunar ta ce bai taɓa zuwa wajen horaswar ba kuma ba a taɓa karɓarsa cikin shirin ba.

Sanarwar ta ce, “Ibrahim Nazifi bai taɓa kasancewa a Depot na Rundunar Sojin Nijeriya da ke Zariya ba, kuma bai taɓa shiga kowanne irin atisayen horaswa ba. Saboda haka, Depot ɗin ba ta da wani bayani na jin rauni ko mutuwarsa yayin horaswa.”

Masu AlakaTRT Afrika - Sojojin Nijeriya sun kashe 'yanta'addan Lakurawa, sun kuɓutar da mutane 62 a Kebbi da Zamfara

Rundunar Sojin ta buƙaci Gwamnatin Jihar Gombe da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da cikakken bincike domin gano a ina, yaushe da kuma a wane yanayi aka ce mutuwar ta faru, tana mai jaddada cewa babu lamari irin wannan da ya faru a cikin Depot ɗin Zariya.

Rundunar ta kuma ce tana sane da cewa atisayen soji na da wahala ta fuskar jiki kuma an tsara shi ne don samar da juriyar jiki, jajircewa da shirye-shiryen yaƙi, Rundunar Sojin Nijeriya ta nuna cewa akwai tsauraran matakan tsaro, kulawar lafiya da hanyoyin rage haɗari domin kare masu horaswa da rage yiwuwar samun rauni.

Depot ɗin ta Zariya ta kuma yi gargaɗi ga jama’a da su guji yaɗa bayanan da ba a tantance ba, tana mai cewa irin waɗannan rahotanni na iya ruɗar da al’umma tare da cutar da martabar Rundunar Sojin Nijeriya ba tare da dalili ba.

Rumbun Labarai
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya
Jami’an tsaron Nijeriya sun kwance wani bam da ‘yan ta’adda suka dasa a Zamfara