| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Hukumar ta bayyana cewa wannan mataki sakon gargadi ne cewa tambarin hukumar ta FRSC alama ce ta mutunci da alhaki mai nauyi.
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki / Others

Hukumar Kiyaye Haddura ta Nijeriya (FRSC) ta sallami jami’ai 43 daga aiki sakamakon laifuffukan da suka aikata.

Jami’an da abin ya shafa sun hada da 31 da aka kora saboda barin wurin aiki ba tare da izini ba, biyar saboda halaye marasa kyau, da kuma bakwai saboda rashin ƙwarewa da saba ƙa’ida yayin aikin sintiri.

Hukumar ta bayyana cewa wannan mataki sakon gargadi ne cewa tambarin hukumar ta FRSC alama ce ta mutunci da alhaki mai nauyi.

“Duk wani jami’i da ya zabi karya ka’idojin wannan cibiyar mai daraja zai fuskanci cikakken hukuncin ladabtarwa na hukumar.” in ji hukumar.

Babban Kwamandan FRSC, Mallam Shehu Mohammed, yayin da yake magana kan lamarin a Abuja, ya bayyana matakin a matsayin tabbaci mai karfi na manufar hukumar ta lamuncewa da rashin ɗa’a da karya ka’idojin aiki.

Mallam Mohammed ya jaddada cewa FRSC a matsayin mai bin tsauraran ƙa’idojin aiki, ba za ta amince da duk wani lamari da zai jawo rashin aminci tsakaninsu da jama’a ko taɓa mutuncin hukumar ko cikas ga ayyukanta.

A cewarsa, barin aiki ba tare da izini ba karya doka ce babba,  da kuma saɓa rantsuwar aiki, musamman a hukuma mai alhakin kare rayukan miliyoyin masu amfani da hanyoyi a kullum.

Ya kara da cewa halaye marasa kyau da rashin ƙwarewa yayin sintiri na rage amincewar jama’a tare da saba wa manyan ƙa’idojin hukumar na ladabi, gaskiya da kwarewar aiki.

Ya ba ‘yan Nijeriya tabbacin cewa hukumar FRSC za ta kara sa ido a cikin gida, ta hanyar ƙarfafa tsarin kulawa, tare da inganta koyar da ɗabi’u masu kyau a dukkan rundunoninta a fadin kasa.

Mallam Mohammed ya kuma bukaci masu ababen hawa su ci gaba da yarda da FRSC tare da tallafa wa kokarinta na tabbatar da hanyoyi masu aminci ga kowa.

Rumbun Labarai
Hukumar DSS ta Nijeriya ta ƙwato bindigogi 676 da harsasai 332,000
INEC za ta yi zaɓen gwaji na Shugaban Ƙasa gabannin zaɓen 2027 na Nijeriya
Ɓarayin daji sun ƙaƙaba harajin naira miliyan 40 kan mazauna wani gari a Sokoto
An lalata makarantu fiye da 1000, an kashe malamai 2,295 a Arewa maso Gabashin Nijeriya - Hukumomi
Annobar da ake zargi mashaƙo ce ta kashe aƙalla mutum 23 a Jihar Filaton Nijeriya
Rundunar sojin Nijeriya ta sanar da kashe ‘yanta'adda 1,500 da kubutar da mutane 777 a watanni biyu
EFCC ta kori ma’aikatanta fiye da 40 saboda zargin cin hanci da rashawa a Nijeriya
Tinubu ya jinjina wa jami’an tsaron Nijeriya kan ceto masu yi wa kasa hidima da aka yi garkuwa da su
Gwamnatin Kano tana bukatar rigakafin cutar mashaƙo miliyan tara daga gwamnatin tarayya
Nijeriya ta nuna damuwa kan abin da ya faru a makwabciyarta Nijar
Shugaba Tinubu zai tafi Turai don fara hutun makonni uku
Babban Sufeton ‘Yansandan Nijeriya ya matsa ƙaimi don ceto waɗanda aka sace a masallacin Jihar Neja
'Yansandan Nijeriya sun kama likitoci kan zargin safarar mutane da cire musu ƙoda
Amurka na shirin janye sojojinta 200 da ta tura Nijeriya
Gwamnatin Nijeriya ta gargaɗi al’ummomi 915 a jihohi 19 kan barazanar ambaliyar ruwa
Sufeta Janar na ’Yansandan Nijeriya ya tura AIG zuwa jihar Neja don ceto masallatan da aka sace
EFCC za ta ba da ladan kashi 5 cikin 100 ga wanda ya ba da bayanai kan kadarorin sata da ke ƙetare
Hedikwatar tsaron Nijeriya ta tattauna da jakadan Saudiyya kan ƙarfafa alaƙar tsaro
Masu garkuwa da mutane a Nijeriya sun tara naira biliyan 7 na kuɗin fansa: Bincike
Ranar Hausa ta Duniya: Harshen Hausa ya gawurta, in ji Shugaba Tinubu