| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Hukumar ta bayyana cewa wannan mataki sakon gargadi ne cewa tambarin hukumar ta FRSC alama ce ta mutunci da alhaki mai nauyi.
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki / Others

Hukumar Kiyaye Haddura ta Nijeriya (FRSC) ta sallami jami’ai 43 daga aiki sakamakon laifuffukan da suka aikata.

Jami’an da abin ya shafa sun hada da 31 da aka kora saboda barin wurin aiki ba tare da izini ba, biyar saboda halaye marasa kyau, da kuma bakwai saboda rashin ƙwarewa da saba ƙa’ida yayin aikin sintiri.

Hukumar ta bayyana cewa wannan mataki sakon gargadi ne cewa tambarin hukumar ta FRSC alama ce ta mutunci da alhaki mai nauyi.

“Duk wani jami’i da ya zabi karya ka’idojin wannan cibiyar mai daraja zai fuskanci cikakken hukuncin ladabtarwa na hukumar.” in ji hukumar.

Babban Kwamandan FRSC, Mallam Shehu Mohammed, yayin da yake magana kan lamarin a Abuja, ya bayyana matakin a matsayin tabbaci mai karfi na manufar hukumar ta lamuncewa da rashin ɗa’a da karya ka’idojin aiki.

Mallam Mohammed ya jaddada cewa FRSC a matsayin mai bin tsauraran ƙa’idojin aiki, ba za ta amince da duk wani lamari da zai jawo rashin aminci tsakaninsu da jama’a ko taɓa mutuncin hukumar ko cikas ga ayyukanta.

A cewarsa, barin aiki ba tare da izini ba karya doka ce babba,  da kuma saɓa rantsuwar aiki, musamman a hukuma mai alhakin kare rayukan miliyoyin masu amfani da hanyoyi a kullum.

Ya kara da cewa halaye marasa kyau da rashin ƙwarewa yayin sintiri na rage amincewar jama’a tare da saba wa manyan ƙa’idojin hukumar na ladabi, gaskiya da kwarewar aiki.

Ya ba ‘yan Nijeriya tabbacin cewa hukumar FRSC za ta kara sa ido a cikin gida, ta hanyar ƙarfafa tsarin kulawa, tare da inganta koyar da ɗabi’u masu kyau a dukkan rundunoninta a fadin kasa.

Mallam Mohammed ya kuma bukaci masu ababen hawa su ci gaba da yarda da FRSC tare da tallafa wa kokarinta na tabbatar da hanyoyi masu aminci ga kowa.

Rumbun Labarai
Nijeriya da Masar na shirin karfafa hadin gwiwa a yaki da miyagun kwayoyi
Matsalar ta'ammuli da miyagun ƙwayoyi tsakanin mata a Nijeriya
Matatar Dangote ta koma amfani da farashin dala don sayar da manta maimakon naira
'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a Jihar Benue da ke tsakiyar Nijeriya, in ji mazauna yankin
Abin da zuwan kasuwar hannun-jarin Nijeriya ta farko a duniya ke nufi
Ɗanyen man da Nijeriya ke samarwa ya kai matakin da ya fi yawa tun watan Yunin 2020
Sojojin Nijeriya sun kashe mai ɗaukar bidiyon ISWAP da gano wasu Larabawa masu horas da ‘yanta'adda
NDLEA ta kama 'yar Afirka ta Kudu kan zargin amfani da ɗanta mai shekara 3 wajen safarar hodar iblis
Hare-haren saman sojin Nijeriya sun kashe gomman 'yanta'addan Boko Haram
Dakarun Nijeriya sun kashe 'yanta'adda' fiye da 300 a Zamfara
Jami'an tsaron Nijeriya sun ceto daliban da aka yi garkuwa da su a Jihar Oyo
Nijeriya ta zo ta farko a duniya a tagomashin kasuwar hannun-jari
Wasu da ake zargi ’yan ISWAP ne da iyalansu sun miƙa wuya ga sojojin Nijeriya
Matatar mai ta Dangote ta fara dakon fetur kyauta zuwa wasu jihohin Nijeriya
Majalisar Dattawan Nijeriya ta buƙaci a soke shirin gyaran hali na tubabbun 'yan Boko Haram
Jihar Legas ta kama mabarata 396, tana tantance bayanansu domin mayar da su jihohinsu na asali
Nijeriya za ta binciki manyan kamfanonin fasaha kan amfani da labaran ƙasar ba bisa ƙa’ida ba
Gwamnatin Nijeriya ta bai wa 'yan ƙasarta damar ƙarshe ta kwashe su daga Afirka ta Kudu
‘Yansandan Nijeriya sun dakile harin ‘yanbindiga a Sokoto
Yadda matsalar tsaron Nijeriya ke ƙara barazana ga wadatar abinci