AFIRKA
2 minti karatu
Jirgi maras matuƙi na RSF ya kashe mutum 30 birnin Al-Fasher na Sudan
Kwamitin 'yan gwagwarmaya na Al-Fasher ya ce jirgin na RSF ya kai harin ne a sansanin 'yan gudun hijira na Dar al-Arqam da ke cikin harabar wata jami'a inda aƙalla mutum 30 suka rasu.
Jirgi maras matuƙi na RSF ya kashe mutum 30 birnin Al-Fasher na Sudan
Masu fafutuka sun ce birnin ya zama wurin da “gawawwaki suke jibge a fili" waɗanda na farar-hula ne masu fama da yunwa.
11 Oktoba 2025

Wani hari da jirgin sama mara matuki ya kashe akalla mutum 30 a wani sansanin 'yan gudun hijira a birnin Al-Fasher da ke yammacin Sudan a ranar Asabar, kamar yadda wata kungiyar masu fafutuka ta bayyana.

Kwamitin gwagwarmaya na Al-Fasher ya ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai hari a sansanin 'yan gudun hijira na Dar al-Arqam da ke cikin harabar wata jami'a.

Kwamitin ya bayyana cewa gawawwaki sun makale a cikin ramin karkashin kasa, yana mai bayyana lamarin a matsayin "kisan kiyashi" tare da yin kira ga al'ummar duniya su shiga tsakani.

Kwamitocin gwagwarmaya na yankin su ne masu fafutuka da ke hada kai wajen bayar da agaji da kuma rubuta rahotanni kan munanan abubuwan da ke faruwa a rikicin Sudan.

‘Gawawwaki jibge a fili’

RSF tana cikin yaki da sojojin gwamnatin Sudan tun watan Afrilu na 2023. Wannan rikici ya kashe dubban mutane, ya raba miliyoyi da muhallansu, kuma ya jefa kusan mutum miliyan 25 cikin yunwa mai tsanani.

Al-Fasher shi ne babban birnin jiha ta karshe a yankin Darfur mai fadi da ya ki fadawa hannun RSF, ya zama sabon filin yaki mai muhimmanci yayin da dakarun RSF ke kokarin karfafa ikon su a yammacin kasar.

Masu fafutuka sun ce birnin ya zama wurin da “gawawwaki suke jibge a fili" waɗanda na farar-hula ne masu fama da yunwa.

Kusan watanni 18 bayan fara yi a birnin Al-Fasher ƙawanya da RSF ta yi, birnin - wanda ke ɗauke da mutum 400,000 waɗanda suka maƙale - kusan komai ya soma ƙarewa.

An rufe wuraren sayar da miya

Abincin dabbobi da iyalai suka dogara da shi tsawon watanni ya yi karanci kuma yanzu ana sayar da shi a kan daruruwan daloli kowace jaka.

Yawancin gidajen abinci na birnin sun rufe saboda rashin abinci, kamar yadda kwamitocin gwagwarmaya na yankin suka bayyana.

Rumbun Labarai
Sojojin Sudan sun harbo jirgi maras matuƙi na RSF a Kordofan ta Arewa
Dakarun Nijar sun cafke muggan makamai da aka yi safararsu daga Libya, sun kama masu safarar ƙwayoyi
RSF ta Sudan ta kai hare-hare a Jihar Khartoum da birnin Atbara bayan amincewa da tsagaita wuta
Paul Biya na Kamaru: Shugaban da ya fi tsufa a duniya ya sha rantsuwar kama aiki karo na takwas
Hatsarin mota ya yi ajalin fiye da mutum 1,000 a Nijar a shekarar 2023, fiye da 12,000 sun jikkata
Sabbin hotunan tauraron dan'adam sun gano alamun 'kaburburan bai-daya a El-Fasher a Sudan
MDD ta yi gargaɗin cewa yaƙin Sudan na gurgunta tattalin arzikin Sudan ta Kudu
Trump ya ce bai kamata Afirka ta Kudu ta kasance cikin G20 ba, ba zai je taronta a Johannesburg ba
'Yan Sudan sun ba da mummunan labarin yi wa mata fyade yayin da suke tserewa daga Al Fasher
An kashe mutane 40 a harin da aka kai wa taron jana'iza a yankin Kordofan na Sudan: MDD
Yadda biranen Afirka mafiya tsafta suke bayyana sauyin da ake samu a nahiyar
Sojojin Ruwa na Ghana sun kama ‘yan Nijeriya 10 da suka ɓuya a jirgin ruwan Panama a Tema
Harin jirgin sama maras matuƙi na RSF ya kashe mutane da dama a lardin Kordofan na Arewa a Sudan
Fiye da mutum 1,500 sun rasa matsugunansu a Sudan sakamakon taɓarɓarewar tsaro: MDD
Dakarun RSF sun kashe mata 300, sun yi wa 25 fyaɗe cikin awa 48 a Al Fasher – Minista
Amurka ta buƙaci a tattauna domin kawo ƙarshen yaƙin Sudan, ba amfani da ƙarfin soja ba
Ana fargabar dubban mutane na cikin 'mummunan hatsari' a birnin Al Fasher na Sudan da RSF ta ƙwace
Shugabar Tanzania Samia Hassan ta lashe zaɓen ƙasar da kashi 97.66 cikin 100
Tchiroma Bakary: Sojojin Kamaru sun yi wa jagoran 'yan adawar kasar rakiya zuwa wuri mai 'aminci'
Kudirin 1325 ya cika shekara 25: Me ya sa dole Afirka ta jagoranci samar da zaman lafiya a duniya