| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Sojojin Nijeriya sun kama 'yan ƙasashen waje 24 a wani samame a Jihar Legas
Rundunar ta ce an gudanar da samamen ne tare da haɗin gwiwar jami'an ƙungiyar sa-kai ta Vigilante Group, bayan samun sahihan bayanan sirri kan kasancewar wasu baƙin-haure da ba su da takardun izinin zama a yankin.
Sojojin Nijeriya sun kama 'yan ƙasashen waje 24 a wani samame a Jihar Legas
Sojojin Nijeriya sun kama 'yan kasashen waje 24

Dakarun Bataliya ta 65 ta Rundunar Sojin Nijeriya sun kama 'yan ƙasashen waje 24 a wani samame da suka kai wani wurin da ake zargin mafakar wasu mutane ne a ƙaramar hukumar Epe ta Jihar Legas, a wani ɓangare na ƙoƙarin da ake yi na yaƙi da aikata laifuka da kuma shige da fice ba bisa ƙa'ida ba.

Rundunar ta ce an gudanar da samamen ne tare da haɗin gwiwar jami'an ƙungiyar sa-kai ta Vigilante Group, bayan samun sahihan bayanan sirri kan kasancewar wasu baƙin-haure da ba su da takardun izinin zama a yankin.

A cewar rundunar, dakarunta sun kai samame wani katafaren fili mai katanga da ke yankin Imokun, a kan titin Odo-Noforija/Poka da ke Epe, inda suka kama maza 15 da mata tara.

Binciken farko ya nuna cewa waɗanda aka kama 'yan ƙasashe shida ne na Yammaci da Tsakiyar Afirka. Sun haɗa da 'yan Kamaru 10, 'yan Togo shida, 'yan Côte d'Ivoire uku, 'yan Jamhuriyar Benin uku, ɗan Burkina Faso ɗaya da kuma ɗan Guinea-Bissau ɗaya.

Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike domin tabbatar da matsayin shigowarsu Nijeriya, dalilin zamansu a ƙasar, da kuma ko suna da hannu a wata haramtacciyar harka.

Haka kuma, jami'an tsaro na ƙoƙarin gano tare da yi wa mai gidan da aka kama mutanen tambayoyi domin ƙarin haske kan yadda suka zauna a wurin da kuma irin ayyukan da suke gudanarwa.

Rundunar ta ce a ranar 16 ga Yulin 2026 ta miƙa dukkan waɗanda aka kama ga Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), reshen Jihar Legas, domin ci gaba da bincike da tantancewa tare da ɗaukar matakan da dokokin shige da fice suka tanada.

Babban Kwamandan Runduna ta 81 ta Sojin Najeriya, Manjo Janar Adebayo Babalola, ya yaba wa dakarun bisa ƙwarewa da nuna ƙwazo wajen gudanar da aikin.

Ya kuma umarce su da su ci gaba da ƙara zage damtse wajen yaƙi da masu aikata laifuka, baƙin-haure ba bisa ƙa'ida ba da sauran barazanar tsaro, tare da jaddada kudurin rundunar na ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare lafiyar al'umma a yankunan da ke ƙarƙashin kulawarta.

Rumbun Labarai
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa  'yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
An saki alƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun daƙile harin daren 'yanta'adda kan sansanin soji
'Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauye Sokoto a Nijeriya
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau
Sojojin Nijeriya sun daƙile yunƙurin 'yanta'adda na garkuwa  da mutane 31 a Borno
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Nijeriya ta lalata makamai guda 2,819 da ta kama a matakin dakile rashin tsaro
'Yansandan InterPol sun tasa ƙeyar ɗan China daga Nijeriya kan safarar namun daji
Nijeriya na da attajirai 7,200 masu arzikin dala miliyan 1 duk da raguwar kuɗi - Rahoto
'Yanbindiga sun kashe Kanar na sojin Nijeriya bayan ya ƙi amincewa su yi garkuwa da shi
Aƙalla mutane 14 ne suka mutu a wani hari da aka kai a jihar Benue ta Nijeriya, in ji jami’an yankin
'Yanta'adda sun kashe aƙalla mutum 30 a wani ƙauye a Kaduna ta Nijeriya
Ana fargabar ɗalibai sun maƙale bayan da gini mai ɗakuna 90 ya rufta da su
Rundunar Sojin Nijeriya ta kama jami'in da ake zargi da sayar wa 'yanta'adda kayan soji
Jami'in da ke kula da harkokin kuɗin ISWAP ya miƙa wuya —Rundunar Sojin Nijeriya
INEC za ta rufe rijistar masu zaɓe ranar Lahadi, 'yan adawa na neman a tsawaita lokacin rijistar