Da misalin ƙarfe 6 na safiyar ranar Alhamis ne aka buɗe rumfunan zabe na babban zaben ƙasar Zambia, inda aka samu dimbin masu kada kuri'a da kuma yanayi na kwanciyar hankali.
Haka kuma tun daga karfe 4 na asuba aka soma ganin layukan mutane a rumfunan zabe, inda matasa da wadanda suka manyanta suka fito da kwansu da kwarkwatarsu don kada kuri'unsu.
'Yantakarar shugaban kasa 14, ciki har da shugaban kasa mai ci Hakainde Hichilema, ne za su fafatawa a babban zaben kasar, a wa’adin mulkin tsawon shekaru biyar masu zuwa.
Hichilema na neman wa'adi na biyu, bayan nasarar da ya samu a shekarar 2021 da kuri'u fiye da miliyan 2.8 wanda ya ba shi damar kayar da shugaban kasa Edgar Lungu na wancan lokacin.
Babban abokin adawan Hichilema
Babban abokin adawan shugaban ƙasar a cikin sauran ‘yantakara 13 a zaben shi ne Brian Mundubile, tsohon minista mai shekaru 55 a gwamnatin jam’iyyar Patriotic Front (PF) wadda ta yi mulki daga 2011 zuwa 2021.
Bayan samun goyon bayan kawancen jam'iyyun adawa, Mundubile ya shiga takarar a watan Mayu kuma yana takara ne a ƙarƙashin sabuwar jam'iyyar NRPUP, wadda ta tattaro goyon bayanta daga jam’iyyar PF.
Kazalika masu kada ƙuri'u za su kuma zaɓi sabbin 'yan majalisa da magajin gari da shugabannin majalisun gundumomi da kuma kansilolin unguwanni.
Ana buƙatar wanda ya yi nasara daga ‘yan takarar shugaban ƙasar ya samu 50 ciki 100 da kuma ɗaya daga cikin jimillar ƙuri'un da aka kada, inda hukumar zaɓe ta ƙasar ta bayyana cewa za a iya sani tare da tantance wanda ya yi nasara nan da ranar Litinin.
Alkawuran yaƙin neman zaɓe
Hichilema, mai shekaru 64, ya lashe zaɓen shugabancin kasar na wa’adin shekaru biyar a 2011 bayan neman kujerar karo na shida kana gangamin yakin neman zaɓensa ya mayar da hankali kan samar da ayyukan yi da kuma wani gagarumin shiri na samar da ababen more rayuwa don tabbatar da sake zaɓe.
Duk da cewa hauhawar farashin kayayyaki ta ragu zuwa kashi 6.8 cikin ɗari a watan Afrilu kuma darajar kuɗin kwacha na ƙasar ta ƙaru, har yanzu mutane da yawa suna fuskantar hauhawar farashin abinci da makamashi.
An daɗe ana kallon ƙasar a matsayin ɗaya daga cikin mafi kwanciyar hankali a Afirka da ke bin tsarin dimokuraɗiyya.
Zaɓe a Zambia ya saba bin ƙa'idojin yankuna, inda jam'iyyar Hichilema ta fi ƙarfi a yankin kudu da yamma, yayin da jam’iyyar PF kuma ta ke riƙe da madafun iko a yankin arewa da Copperbelt.
Ana sa ran fitowar sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a ranar 17 ga Agusta. Sannan ana buƙatar wanda ya yi nasara ya samu fiye da kashi 50 cikin 100 don guje zuwa zagaye na biyu na zaɓen
Kazalika, masu kada kuri’u za su yin zaɓen ‘yan majalisar dokoki 226 a yanzu, karin da aka samu daga kujeru 156 na baya.

























