TURKIYYA
3 minti karatu
Ya kamata amincewar Ƙasashen Yamma da Falasɗinu ta zama silar samar da mafita ta ƙasa biyu: Erdogan
Bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta a Masar, shugaban kasar Turkiyya ya yi kira da ƙasashen duniya su ci gaba da ba da goyon baya kan sake gina Gaza tare da gargadin cewa ka da a manta da matsalar jinƙai.
Ya kamata amincewar Ƙasashen Yamma da Falasɗinu ta zama silar samar da mafita ta ƙasa biyu: Erdogan
Ya kamata amincewar Ƙasashen Yamma da Falasɗinu ta zama silar samar da mafita ta ƙasa biyu: Erdogan
14 Oktoba 2025

Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan a ranar Talata ya bayyana matakan Ƙasashen Yamma na amincewa da Falasdinu a matsayin ginshikan mafita ta tsarin samar da kasashe biyu, maimakon kawai nuna diflomasiyya, kwana guda bayan yarjejeniyar tsagaita wuta a Masar da ta kawo karshen yakin Isra’ila na shekaru biyu kan Gaza.

“A wannan mataki, yana da matukar mahimmanci a ƙara ƙaimi wajen neman mafita ta tsarin kasashe biyu. Muna fatan ganin matakan da Ƙasashen Yamma, musamman Birtaniya da Faransa, suka dauka na amincewa da Jamhuriyar Falasdinu a matsayin ginshikan da za su kai ga mafita ta tsarin kasashe biyu, maimakon kawai ayyukan amincewa.

“Idan ba haka ba, duk wani mataki da aka dauka zai kasance bai cika ba kuma ba zai kai ga burin da ake nema ba.”

Ya sake jaddada cewa kafa wata kasa mai cin gashin kanta, mai ikon mallakar kanta, kuma mai yankin da aka tsara bisa iyakokin shekarar 1967, tare da Gabashin Birnin Kudus a matsayin babban birninta, ita ce kawai mafita.

Masar, Qatar da Turkiyya sun rattaba hannu tare da Shugaban Amurka Donald Trump kan wata takarda game da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza. Trump ya ce kafin rattaba hannu, wannan takarda za ta tsara dokoki da ƙa’idoji.

“Wadannan sa hannun ba kawai alama ba ce — suna nuna jajircewarmu ga zaman lafiya, a matsayin wani bangare na tarihi,” in ji Erdogan.

‘Bai kamata a manta kisan kiyashin Gaza ba’

Shugaban Turkiyya ya kuma soki tarihin Isra’ila na karya yarjejeniyar tsagaita wuta, yana mai cewa duka Turkiyya da Amurka sun ƙuduri aniyar tabbatar da yarjejeniyar zaman lafiya.

“A bayyane yake cewa Isra’ila ba za ta iya cim ma wani sakamako ta hanyar mamaye makwabtanta ba. Yunkurin gwamnatin Netanyahu na daidaita martani kan kisan kiyashi da nuna ƙyama ga Yahudawa ya gaza samar da wani sakamako,” in ji Erdogan.

Ya yi gargadi cewa ba za a manta da halin da mutanen Gaza ke ciki ba, yana mai jaddada cewa ci gaba da mayar da hankali kan diflomasiyya yana da matukar mahimmanci don hana karin bala’in jinƙai.

“Dole ne mu ci gaba da kokarin tabbatar da cewa ba a manta da kisan kiyashin Gaza ba,” in ji Erdogan.

Erdogan ya kuma jaddada mahimmancin diflomasiyya da ake yi tare da Trump, yana mai cewa yana da matukar mahimmanci kuma ya yi alkawarin ci gaba da tattaunawa da irin wannan kulawa.

Gina Gaza yana bukatar goyon baya mai yawa

Shugaban Turkiyya ya ce Ankara tana tattauna da wadanda za su iya shiga cikin aikin sake gina Gaza, yana mai kira da a samu karin goyon baya daga kasashen Gulf, Amurka, da Turai.

Erdogan ya kuma nuna ƙwarin gwiwa cewa za a samu kudade don tabbatar da aiwatar da ayyukan sake gina yankin Falasdinu da aka lalata cikin sauri.

Yayin da yake jaddada halin jinƙai a Gaza, shugaban Turkiyya ya bayyana cewa sake gina Gaza yana da matukar mahimmanci kuma ya yi alkawarin cika bukatun wurin zama na mutanen yankin kafin lokacin sanyi ya iso.

“Za mu yi aiki tukuru don cika bukatun wurin zama na mutanen Gaza kafin lokacin sanyi,” in ji Erdogan a cikin jirgin da ya dawo daga Sharm el-Sheikh, Masar, inda taron zaman lafiya na Gaza ya gudana a ranar Litinin.

Kimanin manyan motoci 350 na agajin jinƙai daga Turkiyya sun shiga Gaza kwanan nan, Erdogan ya lura, yana mai cewa yarjejeniyar Hamas da Isra’ila ta tanadi shigar akalla manyan motoci 600 a kullum.

Rumbun Labarai
Erdogan ya yi Allah wadai da kashe fararen-hula a birnin Al Fasher na Sudan
Za a gudanar da tattaunawa a Istanbul kan yarjejeniyar tsagaita wutar Gaza da matsalolin jinƙai
Tsarin duniya na yanzu ya fi ba da fifiko kan iko fiye da adalci: Babban Daraktan TRT Sobaci
Hamas ba ta da nukiliya, amma Isra'ila na da su: Erdogan ya nemi Berlin ta ɗauki mataki kan Tel Aviv
Ana shirin fara taron TRT World Forum karo na 9 a Istanbul
Cikin hotuna: Yadda aka yi bukukuwa a duk faɗin kasa na cikar Ranar Jamhuriya ta Turkiyya ta 102
Turkiyya ta yi kira a tsagaita wuta nan-take a yaƙin da ake yi a birnin Al Fasher, Sudan
Turkiyya za ta mika wa dakarunta tankar yaki ta Altay da aka samar da yawa a karon farko
Kungiyar ta'addanci ta PKK ta sanar da janyewa baki ɗaya daga Turkiyya
Babu wani lissafin siyasa ko na tsaro da zai yiwu a duniya ba tare da Turkiyya ba: Erdogan
Rumfar Karfe: Fasahar Turkiyya ta cikin gida mai aiki da Ƙirƙirarriyar Basira a sabon zamanin tsaro
Shugaba Erdogan ya shirya ziyartar yankin Gulf don haɓaka alaƙar tattalin arziki da ƙawance
Turkiyya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wutar Afghanistan da Pakistan
An Fara Taron Yaki da Shara na ‘Zero Waste’ a Istanbul karkashin jagorancin Emine Erdogan
Matar Shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta yi kira a bunkasa shigar mata cikin harkokin duniya
Cinikayya tsakanin Turkiyya da Afirka ta wuce $37b ana sa ran ta kai $40b a 2025: Minista
Turkiyya na da rawar da za ta taka a tsaron Turai, ta shirya domin aikin Gaza: Ministan Tsaro
Turkiyya ta yi maraba da amincewar majalisar dokokin TRCN kan ƙudurin samar da ƙasashe biyu
Jami'an Turkiyya da Syria sun gudanar da tattaunawa kan tsaro a Ankara
Turkiya na goyon bayan duk wani ƙoƙari na kawo ƙarshen kisan kiyashi a Gaza: Erdogan