An dakatar da Gasar Kofin Afirka ta Mata a Maroko bayan wasu tawagogi sun fara isa ƙasar

Gasar ta wannan shekara ta Ƙasashen Afirka ta Mata a Maroko, an shirya buɗe ta ranar 17 ga Maris, amma an dakatar da ita da watanni huɗu, cewa Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afrika (CAF).

By
Nijeriya ce mai rike da Kofin Gasar Cin Kofin Mata ta Afirka.

A bana Kofin Ƙwallon Ƙafa na Ƙasashen Afirka na Mata da aka shirya farawa a Maroko ranar 17 ga Maris ya samu tsaiko. An ɗage shi da watanni huɗu, in ji Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ranar Alhamis.

CAF ta faɗa cikin wata sanarwa, cewa ta yanke shawarar sake tsara gasar zuwa tsakanin ranar 25 ga Yuli da 16 ga Agusta, "sakamakon wani yanayi da ba a zata ba". Amma ba a fayyace cikakken bayani ba.

Wasu tawagogin da za su fafatawa a gasar sun riga sun isa Maroko, wadda gasa ce da ke zama hanyar samun cancantar wakilcin Afirka a Gasar Cin Kofin Duniya ta Mata ta 2027, inda ake da guraben ƙasashe shida.

Maroko ta karɓi baƙuncin Kofin Afirka na maza na baya-bayan nan, inda Senegal ta doke masu masaukin baki a wasan ƙarshe ranar 18 ga Janairu.

Ƙasar za ta kuma kasance ɗaya daga cikin masu masaukin baƙi na Gasar Cin Kofin Duniya ta maza ta 2030, tare da Portugal da Spain.