| Hausa
KASUWANCI
2 minti karatu
China za ta soke karɓar harajin fitar da kayayyaki daga ƙasashen Afirka 53
China ta ce daga 1 ga watan Mayu, ƙasar Eswatini ce kaɗai a cikin ƙasashen Afirka za ta ci gaba da biyan harajin kwastam a kan kayayyaki sakamakon har yanzu ƙasar na ci gaba da dangantaka ta diflomasiyya da Taiwan.
China za ta soke karɓar harajin fitar da kayayyaki daga ƙasashen Afirka 53
Shugaban kasar China, Xi Jinping. / Reuters
14 awanni baya

Shugaban kasar China, Xi Jinping, a ranar Asabar ya ce daga 1 ga watan Mayu, za a soke duk wani harajin fitar da kayayyaki zuwa duka ƙasashen, banda ƙasa ɗaya, kamar yadda kafafen watsa labarai na ƙasar suka ruwaito.

Dama tuni China ta soke kaɓar harajin ko sisin kwabo daga ƙasashen Afirka 33, inda a bara ta sanar da cewa za ta ƙara faɗaɗa tsarin zuwa ƙasashe 53 na Afirka.

China ita ce babbar abokiyar kasuwanci ta Afirka kuma babbar mai gudanar da ayyukan ababen more rayuwa a nahiyar ta hanyar shirin 'Belt and Road'.

Daga 1 ga Mayu, ba za a karɓi harajin kwastam ba daga dukkan kasashen Afirka sai Eswatini, wadda ke ci gaba da dangantaka ta diflomasiyya da Taiwan.

China na ikirarin tsibirin a matsayin mallakinta inda ta ce akwai yiwuwar za ta iya amfani har da ƙarfi domin ƙwace iko da shi.

Yawancin ƙasashen Afirka suna kara duba komawa hulɗa da China da sauran abokan kasuwanci tun bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ya ƙaƙaba manyan haraji a duk duniya a bara.

Xi ya ce yarjejeniyar ba shakka za ta samar da sabbin damammaki ga ci gaban Afirka, inda yake sanar da ranar da za a cire wannan haraji a daidai lokacin da shugabannin na Afirka ke taron Ƙungiyar Tarayyar Afirka a Ethiopia.