| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Uganda za ta tura sojoji domin aiki a yankin Gaza
Ministan Tsaro Kiryowa Kiwanuka ya bayyana ƙarfin sojojin Uganda inda ya ba da misalin da ayyukan zaman lafiya da suka je kasashe kamar Somalia
Uganda za ta tura sojoji domin aiki a yankin Gaza
Dakarun Uganda sun je ayyukan wanzar da zaman lafiya a kasashe daban-daban na Afirka.

Hukumomin Uganda sun samu amincewar majalisar dokoki na tura sojoji zuwa Gaza a matsayin wani ɓangare na rundunar ƙasa da ƙasa da Shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar don tabbatar da tsaron yankin bayan mummunan yaƙin kisan ƙare-dangi na Isra’ila.

Wannan ƙuduri, wanda ministan tsaro ya gabatar, shi ne farkon alamar da Uganda ta nuna a bainar jama'a game da sha'awarta ta shiga Rundunar Tsaro ta Duniya a Gaza.

Maroko ma ta yi alƙawarin ɗaukar sojoji tare da tura su aikin.

Ba a fayyace dalilin da ya sa Uganda ta amince ta tura sojoji zuwa Gaza ba, ko kuma idan akwai wani abu da ya shafi hakan, kuma wasu 'yan majalisar adawa nan da nan suka yi tambaya game da dalilin Uganda na yanke wannan shawara.

Ministan Tsaro, Kiryowa Kiwanuka, wanda ke neman goyon bayan 'yan majalisa, ya ambaci ƙarfin sojojin Uganda da ya samo asali daga aikin wanzar da zaman lafiya a ƙasashe kamar Somalia.

Jure zaman lafiya

Rundunar, wadda Kwamitin Zaman Lafiya na Trump ya gabatar a watan Fabrairu, za ta kasance ƙarƙashin jagorancin Manjo Janar Jasper Jeffers na Amurka, wanda ya ce a watan Mayu rundunar mai karfin sojoji 20,000 za ta tabbatar da "makoma mai kyau da zaman lafiya mai ɗorewa."

A cewar wannan yarjejeniyar, za a tura Rundunar Zaman Lafiya ta Duniya zuwa Gaza bayan kammala janye sojojin Isra'ila a mataki na farko.

Yarjejeniyar, wani ɓangare ne na yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cim ma a bara, kuma ta yi kira ga Isra'ila da ta dakatar da ayyukanta na soji da kuma ga Hamas da ƙawayenta a Gaza su dakatar da duk wani aikin 'yanbindiga.

Yarjejeniyar ta kuma bayyana a takaice yadda tsarin janye dakarun zai kasance.

Bayan an fitar da bayanai kan yarjejeniyar, Isra'ila ta ce tana da "matsalar tsaro mai tsanani" kuma ta bayyana wa Amurka su.

Hare-haren Isra'ila sun kashe mutane 1,250 tun lokacin da aka cim ma yarjejeniyar tsagaita wuta a watan Oktoba.