Shugaban ƙasar Djibouti, Ismaïl Omar Guelleh, ya sake samun nasarar lashe zaɓe a karo na shida, bayan da sakamakon hukuma ya nuna ya samu kashi 97.81 na ƙuri’un da aka kaɗa a zaɓen ranar Jumma’a.
Ya fafata ne da ɗan takara guda ɗaya tilo, Mohamed Farah Samatar, tsohon ɗan jam’iyya mai mulki, a wata takara da masana ke gani ba ta da wani babban ƙalubale na gaske.
Akai-akai ƙungiyoyin hamayya kan ƙaurace wa zaɓe, suna masu nuni da takura wa ’yancin siyasa.
Gwamnati ta musanta zarge-zargen tafka maguɗi ta fuskoki daban-daban, sannan ta yi watsi da su musamman kan yadda tsarin zaɓen ya gudana.
Guelleh, mai shekaru 78, ya jagoranci ƙasar da ke yankin Kusurwar Afirka tun shekarar 1999, lokacin da ya gaji Hassan Gouled Aptidon, wato shugaban da ya kafa ƙasar Djibouti.
A watan Oktoban da ya gabata, majalisar dokoki ta kaɗa ƙuri’ar soke ƙa’idar shekaru 75 da aka gindaya a baya ga ’yan takarar shugaban ƙasa, sannan ta soke bukatar yin ƙuri’ar raba-gardama da ake buƙata a baya don amincewa da sabon kundin tsarin mulki.
Guelleh ne da kansa ya shigo da wannan ƙa’idar shekaru a shekarar 2010, a matsayin ɓangare na sauye-sauyen da suka soke ƙa’idar iyakance yawan wa’adin da shugaba zai yi, yayin da aka rage tsawon kowane wa’adi daga shekaru shida zuwa biyar.






