| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Fadar ta ce za a tarbi Shugaba Tinubu da matarsa, Oluremi Tinubu, a Fadar Windsor, a yammacin London, inda Sarki Charles da Sarauniya Camilla za su tarbe su.
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
London da Abuja sun kulla wani kawance ta dabaru a watan Nuwamban 2024 don ƙarfafa haɗin kansu kan harkokin tattalin arziki, shige da fice, da tsaro. / Others
15 awanni baya

Sarkin Charles na uku na Birtaniya zai karɓi baƙuncin Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, a wata ziyara ta ƙasa da ƙasa da zai kai ta yini biyu zuwa Birtaniya a ranakun 18–19 ga Maris, in ji Fadar Buckingham a wani bayani a ranar Asabar.

Fadar ta ce za a tarbi Shugaba Tinubu da matarsa, Oluremi Tinubu, a Fadar Windsor, a yammacin London, inda Sarki Charles da Sarauniya Camilla za su tarbe su.

London da Abuja sun kulla wani kawance ta dabaru a watan Nuwamban 2024 don ƙarfafa haɗin kansu kan harkokin tattalin arziki, shige da fice, da tsaro.

Nijeriya wadda ke yammacin Afirka na fama da ta'addanci tsawon shekaru a arewa maso gabas, da kuma garkuwa da mutane don neman kuɗin fansa daga ƙungiyoyin ta’addanci a arewa maso yamma da tsakiyar ƙasar.

A ranar Juma'a, Ma'aikatar Tsaron Nijeriya ta ce ƙasashen biyu suna shirin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro jim kaɗan bayan kisan mutane fiye da 160 a Jihar Kwara da ke tsakiyar ƙasar wanda Shugaba Tinubu ya danganta ga 'yan ta'adda.

Azabtarwar mulkin mallaka

Nijeriya ƙasa ce wadda Birtaniya ta yi wa mulkin mallaka kuma mamba ce ta ƙasashen renon Ingila inda take da aƙalla mutum miliyan 230, kuma tana daga cikin manyan tattalin arzikin nahiyar.

Ko da yake Charles ya tarbi Shugaba Tinubu a watan Satumban 2024, wannan tafiya za ta kasance ziyarar ƙasa ta farko a hukumance daga shugaban Nijeriya zuwa Burtaniya cikin shekaru 37.

Charles ya ziyarci Nijeriya sau huɗu a lokacin da yake Yarima na Wales kafin rasuwar mahaifiyarsa, Sarauniya Elizabeth II, a 2022.

A ranar Juma'a, kotun Nijeriya ta umarci gwamnatin Birtaniya da ta biya fam £420 miliyan ga iyalan masu haƙar ma'adinan da aka kashe a 1949 ta hannun masu mulkin mallaka, bayan da suka yi zanga-zangar yanayin aikin su da albashin da ba a biya su ba ta hanyar mamaye ma'adinan da suke aiki a ciki.

Wannan kisan dai yana cikin jerin azabtarwar da Birtaniya ta aikata a lokacin mulkin mallaka a Nijeriya da sauran sassan Afirka.

Rumbun Labarai
Nijeriya ta ƙaddamar da tsarin tattalin arzikin halal domin bunƙasa arzikin ƙasar
Solar Halo: Yadda mazauna birnin Jos a Nijeriya suka ga al'ajabin rabuwar Rana gida uku
Kotu ta umarci Birtaniya ta biya diyyar £420m ga iyalan masu haƙar kwal 21 a Nijeriya
NCC ta gargaɗi masu gini da aikin hanya kan lalata layukan sadarwa na ƙarƙashin ƙasa a Nijeriya
Jamhuriyar Benin da AU sun yi Allah wadai da harin ta'addanci da ya kashe mutum 170 a Nijeriya
NNPC na tattaunawa da kamfanin China domin farfaɗo da matatun man Nijeriya
Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar soji Jihar Kwara
Mummunan harin ta'addanci ya kashe fiye da mutum 160 a Jihar Kwara ta Nijeriya
Annobar cizon maciji a Nijeriya: Abin da ya sa mutuwar mawaƙiya Nwangene ta zama kiran ɗaukar mataki
Rundunar sojin Amurka tabbatar da tura 'wata ƙaramar tawaga' Nijeriya
'Yan fashin daji sun kashe mutum 30 a hare-haren da suka kai a Katsina da Kwara
Kotun Nijeriya ta tuhumi tsohon ministan shari'a Malami da laifukan ta'addanci
An gurfanar da mutum 9 a kotu bisa zargin kisan mutum 150 a Yelwata na jihar Benue a 2025
Gomman masu ibada da ake fargaba an yi garkuwa da su daga cocin Kurmin Wali sun koma gida
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan Boko Haram, Abu Khalid a Sambisa
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan ISWAP a arewa maso gabas
Daga tsaro zuwa kasuwanci: Abin da ya sa juyawar Nijeriya zuwa Turkiyya ke da muhimmanci
Nijeriya da Saudiyya sun sanya hannu kan yarjejeniyar ɗaukar ma'aikata a karon farko
Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za ta warware rikicin Masarauta
‘Yansandan Nijeriya sun ƙwato kwamfuta 400, sun kama ɓarayin airtime na Naira biliyan 7.7