| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Uganda za ta sallami majinyacin Ebola na ƙarshe
Za a iya ayyana ƙasar a matsayin wadda ba ta da Ebola idan ba a samu sabbin rahotanni na mutanen suka kamu da cutar ba a cikin kwanaki 42 na sa idon Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO).
Uganda za ta sallami majinyacin Ebola na ƙarshe
Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi kira da a tallafawa yankuna don yakar cutar Ebola

Uganda na shirin sallamar majinyacin Ebola na ƙarshe a ranar Alhamis, wanda hakan ke nuna rana ta farko ta soma ƙidayar kwanaki 42 kafin a ayyana ƙasar a matsayin wacce ba ta da cutar Ebola, kamar yadda mai magana da yawun gwamnatin ƙasar ya bayyana.

A ƙarƙashin tsarin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), za a iya ayyana ƙasa a matsayin wadda ta fita daga cikin jerin masu ɗauke cutar Ebola idan ba a samu sabbin alƙaluma na mutanen da suka kamu da cutar ba a tsawon kwanaki 42 a jere, bayan sallamar mutum na ƙarshe wanda aka tabbatar ya warke daga cutar.

 Uganda ta kai matakin ƙarshe na ɓarkewar cutar

Ma'aikatar Lafiya ta Uganda ta ce marasa lafiya daga cutar Ebola 17 sun warke, inda mutum ɗaya da aka keɓe ya rage kana an samu rahoton mutuwar mutane biyu.

Sannan an samu mutane biyar da suka kamu da cuta a cikin gida, yayin da 15 kuma suka shiga ƙasar da cutar.

Mai magana da yawun gwamnatin ƙasar Alan Kasujja ya ce za a sallami majinyaci na ƙarshe daga Asibitin Kula da Lafiya na Mulago da ke babban birnin Kampala, ranar Alhamis.

"Idan hakan ta faru, Uganda za ta soma ƙirga kwanaki, " kamar yadda Kasujja ya wallafa a shafinsa na X.

Ya ƙara da cewa "Idan kwanaki 42 suka wuce ba tare da an samu wani sabon mutum da ya kamu da cutar ba, Hukumar WHO za ta ayyana mu a matsayin ƙasar da ba ta da cutar Ebola."

Ƙasar da aka fi samu barkewar cutar, wadda WHO ta ayyana ta kai matakin gaggawa ta lafiyar jama'a wato Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC) a watan Mayu, ta samu mutane 2,011 da aka tabbatar sun kamu da cutar da mutuwar mutane 754 ya zuwa ranar Labaran nan, a cewar alƙaluman gwamnatin ƙasar ta Congo.

Duk waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar suna da alaƙa da nau'in ƙwayar cutar Bundibugyo da ba a saba gani ba, wanda WHO ta bayyana a matsayin annobar cuta ta uku mafi girma a tarihi.

Rumbun Labarai
Mutane fiye da 4,000 ne suka kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo - Gwamnati
Kwamitin tattaunawa na Libiya ya cim ma matsaya kan tsarin ɗaukar shugaban hukumar zaɓe
Gargadin shugabannin Afirka kan cin abinci a makare da illolin shan siga da giya
Shugaba Biya na Kamaru ya yi sauye-sauye a shugabancin sojin ƙasar
Ghana ta amince da ɗaurin shekara 20 ga duk wanda ya mayar da gonar koko zuwa wani abu daban
Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren 'yanta'adda
‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati
Fitacciyar mawaƙiyar Afirka Ta Kudu ta soke kalankuwarta a Legas bayan an kori baƙi daga ƙasarta
Gwamnatin Ghana ta amince da shawara ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa
Adadin 'yan ci-ranin da suka rasu ya kai 19 bayan dubbai sun tsallaka zuwa yankin Ceuta na Sifaniya
Biranen Afirka 25 da Amurka za ta rufe ayyukan bayar da biza daga ranar 1 ga Agustan 2026
Siyasar Kamaru: Ina Shugaba Paul Biya ya shiga?
Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 kan zargin ɓoye shi don haddasa ƙarancinsa
Hukumomin Libya a Benghazi sun kori baƙin-haure fiye da 117,000 daga ƙasar
Mutumin da ya fi kowa tsawo a Ghana Awuche ya rasu
Chadi ta sanar da shirin fita daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC)
An gudanar da zanga-zanga a Tripoli saboda tsadar rayuwa da tabarbarewar ayyukan gwamnati
Ƙarin ma'aikatan jinya sun shiga yajin aiki yayin da cutar Ebola ta kama kusan mutum 3,000
Yara na cikin waɗanda aka kashe a harin jirgi marar matuƙi a wata kasuwar Sudan
Jam'iyyar da ke mulki a Kamaru ta yi zama kan dogon hutun Shugaba Biya da ya jawo tambayoyi