| Hausa
TURKIYYA
3 minti karatu
Babu wanda ke son sake ɗaukar hoto da Netanyahu, in ji Ministan Harkokin Wajen Turkiyya
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya ya ce manufofin Netanyahu, da suka janyo mutuwa da rushe gine-gine a yankin, sun mayar da Isra’ila saniyar ware.
Babu wanda ke son sake ɗaukar hoto da Netanyahu, in ji Ministan Harkokin Wajen Turkiyya
Fidan ya ce kar a yi wa matsayin Turkiyya kallon wani abu na bijirewa. / AA
16 Janairu 2026

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ƙara mayar da ƙasarsa saniyar ware ta hanyar dabbaka manufofin soji masu tsauri waɗanda suka haifar da mutuwa da barna a yankin, in ji Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan.

Da yake magana da manema labarai a Istanbul ranar Alhamis, Fidan ya ce a cikin yanayin da ake ciki, daidaita dangantaka da Isra'ila ya zama abin da ba zai yiwu ba - ba kawai ga Turkiyya ba, har ma ga ƙasashe da yawa a duniya.

"Muddin hakan ya ci gaba da faruwa, ba zai yiwu ba mu gyara alaka da Isra’ila, ba mu ba ma har da wasu ƙasashe da yawa," in ji Fidan, yana mai nuni da ayyukan soji da Isra'ila ke ci gaba da yi.

Jawabinsa ya nuna wata babbar gaskiyar diflomasiyya inda shugabancin Isra'ila ke fuskantar ƙaruwar adawa, ba kawai daga gwamnatoci ba, har ma daga ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da aka zaɓa a Turai.

Fidan ya nuna rashin amincewar shugabannin Turai na yin mu'amala da Netanyahu a bainar jama'a, yana mai lura da cewa kaɗan ne kawai, idan ma akwai, ke son tafiya zuwa Isra'ila ko a ɗauki hotonsu tare da shi.

"Babu wanda zai je (Isra'ila)," in ji shi. "Me ya sa ba za su je ba? An zaɓi shugabannin Turai. Sun san cewa ɗaukar hoto tare da shi ba abu ne mai kyau ba a kwanakin nan."

Ministan na Harkokin Wajen Turkiyya ya bayyana wannan nesanta a matsayin shaida na karuwar killacewar diflomasiyya ta Isra'ila.

Ya yi tambaya ko da gaske Netanyahu zai iya ziyartar kowace ƙasa da ba Amurka ba, yana mai nuna cewa ko da ƙawayensa na ƙud-da-ƙud na ƙara taka tsantsan.

"Zai iya zuwa ko ina bayan Amurka? Ba zai iya ba. Wataƙila zai zo Girka" in ji Fidan.

Fidan ya ce bai kamata a ɗauki matsayin Turkiyya game da Isra'ila a matsayin wani abu da ya wuce gona da iri ko kuma ra'ayi da ke haifar da akida ba.

Madadin haka, ya bayyana shi a matsayin wani ɓangare na martani mai faɗi da aka yada a tsakanin al'ummomin duniya.

"Wannan ba shi ne matsayinmu kawai ba," in ji shi. "Manufa ce da al'ummomin duniya suka bayyana, waɗanda ke da tunani da ɗabi'u iri ɗaya, a cikin tsari da salo daban-daban."

Fidan ya ce wasu ƙasashe sun zaɓi bayyana adawarsu ga Isra'ila a fili, yayin da wasu suka zaɓi yin amfani da hanyoyi na nutsuwa na rabuwa da Isra'ila, suna guje wa ziyarar shugabanninsu zuwa kasar.

Ya kuma bayyana cewa wannan bambancin salo, ba ya canza ainihin saƙon da ake aika wa shugabannin Isra'ila.

 

Rumbun Labarai
Adadin jama'ar Turkiyya ya kai miliyan 86 a 2025 yayin da jama'ar ƙasar ke ƙara yawa
Matar Shugaban Turkiyya da Sarauniyar Jordan sun ƙara jaddada ƙawance a Istanbul
Turkiyya ta kama jami'an Mossad na Isra'ila biyu a Istanbul kan leƙen asiri
Shugaba Erdogan ya tuna da girgizar ƙasa, ya ce ‘Turkiyya ta cika alkawarinta‘ na sake gina gidaje
Turkiyya ta bunƙasa taimakon da ta ke ba Somaliya na sojojin sama da ƙasa don yaƙi da ta'addanci
Shugaban Turkiyya Erdogan ya gana da Yarima Mai Jiran Gado na Saudiyya Mohammed bin Salman a Riyadh
Shugaban Turkiyya zai ziyarci Saudiyya da Masar a cikin wannan makon
Fidan na Turkiyya ya gargaɗi Amurka kan kai wa Iran hari, ya ce Tehran a shirye take ta tattauna
Zaman lafiyar Iran na da muhimmanci ga tsaron yankin: Turkiyya
Turkiyya da Nijeriya sun ƙudiri aniyar kyautata alaƙar kasuwanci, zuba jari da tsaro
Erdogan da Trump sun tattauna kan Syria da Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza
Turkiyya ta goyi bayan Nijeriya a yaƙi da ta'addanci yayin da Erdogan ya karbi baƙuncin Tinubu
Ziyarar Tinubu a Turkiyya: Muhimman abubuwa a tsarin dangatakar Nijeriya
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwaransa na Nijeriya Tuggar
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya da takwaransa na Nijeriya za su gana kan cinikayya da tsaro
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hidan ya yaba da "Kwamitin Zaman Lafiya" na Gaza
Turkiyya ta ɗauki dukkan yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da mahimmanci: Erdogan
Fidan na Turkiyya zai halarci bikin sa hannu na 'Hukumar Zaman Lafiya' ta Gaza a Switzerland
An tono makarantar Islamiyya mai shekara 900 yayin aikin sabunta birni a yankin Anatolia a Turkiyya
‘Syria ta ‘yan Syria ce’: Erdogan ya yaba da yarjejeniyar zaman lafiya ta Damascus