| Hausa
TATTALIN ARZIKI
2 minti karatu
ECOWAS ta sanya hannu kan yarjejeniyar tallafa wa aikin bututun iskar gas na Nijeriya da Morocco
An tsara hanyar bututun ne don jigilar iskar gas mita cubic biliyan 30 (bcm) a shekara guda daga Nijeriya zuwa Marocco ta hanyar ƙasashe 13 da ke yankin yammacin Afirka, a cewar wata sanarwa haɗin gwiwa tsakanin Morocco da Nijeriya.
ECOWAS ta sanya hannu kan yarjejeniyar tallafa wa aikin bututun iskar gas na Nijeriya da Morocco
An tsara hanyar bututun ne don jigilar iskar gas kyubik mita biliyan 30 a shekara guda daga Nijeriya zuwa Maroko

Mambobin ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka (ECOWAS) sun sanya hannu kan wata yarjejeniya tsakanin gwamnatoci ƙasashen a ranar Lahadi a Freetown don tallafa wa ayyukan bututun iskar gas na Nijeriya da Morocco Atlantic, a cewar wata sanarwar haɗin gwiwa tsakanin Maroko da Nijeriya.

An tsara hanyar bututun ne don jigilar iskar gas kyubik mita biliyan 30 (bcm) a shekara guda daga Nijeriya zuwa Maroko ta hanyar ƙasashe 13 da ke yammacin Afirka, a cewar sanarwar haɗin gwiwa wadda hukumar sinadarin hydrocarbon da haƙo mai ta Maroko ONHYM da kamfanin mai na Nijeriya NNPC suka fitar.

Daga cikin adadin, za a samar da kyubik mita 15 a kowace shekara ga kasuwannin Maroko da Turai ta hanyar bututun da ya haɗa Maroko da ƙasar Sifaniya, in ji sanarwar.

An amince da yarjejeniyar shekaru goma da suka wuce, tsakanin Sarkin Maroko da tsohon shugaban Nijeriya marigayi Muhammad Buhari, kuma an tsara bututun zai kai tsawon kilomita 6,900 kuma an ƙiyasta za a kashe dala biliyan 25 a aikin.

Tuni dai aka kammala matakin bincike da tsare-tsaren injiniyoyi a matakin farko (FEED) na aikin.

A watan Afrilu, ONHYM ta shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa an tsara aikin ne don haɓaka haɗin kan tattalin arziki a faɗin Yammacin Afirka ta hanyar faɗaɗa samar da wutar lantarki da kuma sauƙaƙa ci-gaban masana'antu da haƙar ma'adinai, tare da taimaka wa Maroko ta sanya kanta a matsayin hanyar makamashi tsakanin Afirka da Turai.

Mataki na gaba zai mayar da hankali kan sanya hannu a wata yarjejeniya tsakanin Maroko da Mauritania mai arzikin iskar gas a gaban shugaban Nijeriya, a cewar sanarwar.