| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Turkiyya ta gano kayan tarihi 76 da aka yi amannar na Nijeriya ne da za a mayar da su gida
Wata sanarwa ta ce Poroy yana fatan za a iya sanya hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa tsakanin Turkiyya da Nijeriya a lokacin ziyarar da Shugaba Bola Tinubu zai kai Turkiyya.
Turkiyya ta gano kayan tarihi 76 da aka yi amannar na Nijeriya ne da za a mayar da su gida
Jakadan, ya yi maganar a ranar Alhamis lokacin da ya ziyarci Ministar Fasaha, Al'adu, Yawon Bude Ido Hannatu Musa Musawa, a Abuja / Others
23 Janairu 2026

Turkiyya ta gano kayayyakin tarihi guda 76 na katako da ƙarafa da ake kyautata zaton mallakin Nijeriya ne, wanda hakan ke share fagen mayar da su gida da kuma ƙarfafa alaƙar al'adu tsakanin ƙasashen biyu, in ji jakadan Turkiyya a Nijeriya, Mehmet Poroy.

Jakadan, wanda ya yi magana a ranar Alhamis lokacin da ya ziyarci Ministar Fasaha, Al'adu, Yawon Bude Ido da Tattalin Arzikin Kirkire-kirkire ta Nijeriya, Hannatu Musa Musawa, a Abuja, ya ce tattaunawa kan dawo da su za ta fara ne lokacin da Nijeriya ta gane su kuma ta ce natan ne.

Wata sanarwa ta ce Poroy yana fatan za a iya sanya hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa tsakanin Turkiyya da Nijeriya a lokacin ziyarar da Shugaba Bola Tinubu zai kai Turkiyya.

"Ministanmu na Al'adu da Yawon Buɗe ido ya gano abubuwa 76 na katako da ƙarfe waɗanda suke ganin na Nijeriya ne. Mun sami bayanai game da waɗannan kayan tarihi a watan Mayun da ya gabata kuma muna son a dawo da su.

"Muna fatan sanya hannu kan yarjejeniyar haɗin gwiwa a lokacin ziyarar Shugaban Nijeriya zuwa Turkiyya. Za mu inganta fahimtar al'adu da haɗin gwiwa a tsakaninmu," in ji shi.

Ambasada Poroy ya tattauna kan shirye-shiryen kafa cibiyar al'adu a Nijeriya don bunkasa fasahar gargajiya da kuma ilmantar da matasan Nijeriya.

Hannatu Musawa ta lura da muhimmancin kammala yarjejeniyar, tana mai kira ga jami'ai da su hanzarta aiwatar da wannan tsari.

Ministar ta nuna sha'awar Nijeriya ta hada kai da Turkiyya kan ayyukan masana'antar fina-finai, musayar al'adu, da kuma karfafa mata a fannin ado.

Ta jaddada rawar da Nijeriya ke takawa a tattaunawar al'adu ta duniya, musamman a yankin Kudu maso Gabashin Duniya, da kuma yiwuwar hadin gwiwar Turkiyya da Najeriya don inganta fahimtar al'adu da ci gaban tattalin arziki.

 

Rumbun Labarai
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya