| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Yakin Sudan: Yara na daga gomman da aka kashe a arangamar makonni biyu a Kordofan
Ma’aikatan lafiya na yankin sun ce shaidar waddanda suka kubuta a Kudancin Kordofan na nuna cewa mata manya biyar da yara kanana tara na daga cikin wadanda aka kashe a makonni biyun da suka gabata.
Yakin Sudan: Yara na daga gomman da aka kashe a arangamar makonni biyu a Kordofan
Jihohin Kordofan uku - Arewa, Yamma da Kudu tsawon makonni sun fuskanci kazamin rikici tsakanin sojojin Sudan da mayakan RSF. / Reuters

Tsananin rikici a Kudancin Sudan ya yi ajalin akalla mutane 61, ciki har da yara kanana tara, in ji wata kungiyar ma’aikatan lafiya a ranar Laraba, rikicin da yake wani bangare na yakin da ya afka wa kasar tun 2023.

Kungiyar Sudan Network, wadda ke sanya ido kan yawaitar asara a yakin, ta ce a farkon wannan watan ne fada ya barke tsakanin Mayakan Kungiyar ‘Yantar da Sudan da ‘yan kabilar Otoro a garin Kauda, da ke Kudancin Kordofan.

Shugaban ‘yan tawaye Abdulaziz Al-Hilu, wanda ke jagorantar kungiyar ya hade mayakansa da na RSF, kungiyar da ke yakar sojojin Sudan.

Yakin Sudan da ya shiga shekara ta hudu ya bar sojojin rike da iko da arewaci, gabas da tsakiyar kasar, ciki har da yankunan da ke dauke da tashoshin jiragen ruwa.

Shaida daga wadanda suka tsira

Sanarwar da aka fitar daga kungiyar likitocin ta bayar da bayan shaidu da aka tattara a Kudancin Kordofan, inda wadanda suka tsira suka ce an kashe mata biyar da yara tara a rikicin na makonni biyu.

Mohammed Elsheikh, kakakin kungiyar, ya fada wa AP cewa rashin kyakkawan yanayin sadarwa ya sanya da wahala a iya fayyace cikakken adadin, wanda na iya zama sama da haka saboda ana ci gaba da arangama.

Kungiyar likitocin ta kuma ce mayakan ‘yan tawayen sun kona gidaje da shaguna tare da sace kayayyaki.

Wadanda suka tsira sun ce an kai wa fararen-hula hari ba tare da bambancewa ba.

Kungiyar ta kuma yi gagaɗin cewa a yankin Kauda an samu kai munanan hare-hare kuma babu hanya mai kyau da za a bi domin kwashe fararen-hula.

An kai wa fararen-hula hare-hare

A yankin Dilling, wani gari a Kudancin Kordofan, hari da manyan tankoki daga RSF ya kashe mutane bakwai da jikkata wasu 17, kamar yadda wani asibitin yankin ya bayyana.

Daraktan asibitin Umm Bakhita , Omran Teia ya fada wa AP cewa mayakan sun kai wa fararen-hula hari.

Majalisar Dinkin Duniya da wasu kungiyoyi takwas sun zargi bangarorin Sudan biyu da ke rikici da juna da aikata munanan ayyuka, ciki har da karar da kabilu, kisan kare-dangi da cin zarafin mata da cusguna wa fararen-hula.

Kungiyoyin agaji sun ce adadin na iya fin haka sosai a yayin da ba a iya isa ga yankuna da dama da ake rikici a cikin su a kasar.

Rumbun Labarai
Mali ta haramta hawa babura a wajen birane saboda hare-haren ta'addanci
Tawagar kwallon DRC na neman abokiyar karawa bayan Sifaniya ta fasa buga wasa da su saboda Ebola
'Yan Nijeriya da Mozambique da Laberiya na cikin mutum  21 da gobarar otel ta kashe a New Delhi
Shugaban Nijar Abdourahamane Tiani ya fara ziyarar aiki a Turkiyya
Nijar da Benin sun ƙaddamar da kwamitin da zai sa ido kan iyakokin ƙasashen biyu
Manyan attajiran Afirka da kuma nauyin talaucin da nahiyar ke fama da shi
Malawi za ta kwashe 'yan ƙasarta daga Afirka ta Kudu saboda matsalar rikicin ƙyamar baƙi
Dalibai tara sun gurfana a gaban kotu kan tayar da gobara a wata makaranta a Kenya
Mutane da yawa sun fito da wuri don kaɗa kuri'a a babban zaben Habasha
Shugaban WHO ya ziyarci cibiyar Ebola yayin da cutar ke ƙara ƙamari
Amurka ta aike wa Nijar kayan aikin soja da darajarsu ta kai dala miliyan 2.3 duk da takun-saƙa
Ɗalibai 16 sun rasu sakamakon gobara a wata makarantar 'yanmata a Kenya
Ghana ta kwashe 'yan ƙasarta 300 daga Afirka ta kudu yayin da ake zanga-zanga kan baƙin haure
Mutane uku sun mutu bayan motar fasinja ta yi karo da giwa a gandun dajin Uganda
Shugaban Senegal Faye ya naɗa sabon firaminista da zai maye gurbin Sonko
Adadin mutanen da Ebola ta kashe a Jamuhuriyar Kongo ya wuce 200
Shugaban Senegal Faye ya sallami Firaministansa Ousmane Sonko
Kenya za ta rage farashin man dizel bayan zanga-zangar da aka yi kan tsadar makamashi
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar za ta ƙayyade kuɗin gidajen haya
Sierra Leone ta amince ta karɓi kashin farko na waɗanda aka taso ƙeyarsu daga Amurka