| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
2 minti karatu
Iran ta yi atisaye a mashigin tekun Hormuz ranar jajiberin tattaunawarta da Amurka a Geneva
Atisayen na zuwa ne cikin wnai yanayi na tayar da jijiyar wuya tsakanin Tehran da Washington bayan Amurka ta yi tanadin soji a yankin mashigar ruwa.
Iran ta yi atisaye a mashigin tekun Hormuz ranar jajiberin tattaunawarta da Amurka a Geneva
(TSOHON HOTO) Bakin tekun Iran daga sama da kuma tashar jiragen ruwan Bandar Abbas a sashen tekun Hormuz / Reuters / Reuters
17 Fabrairu 2026

Rundunar juyin-juya-halin Iran (IRGC) ta fara wani atisayen soji a mashigin tekun Hormuz, kwana ɗaya kafin a fara zagaye na biyu na tattaunawa a kaikaice tsakanin ƙasar da Amurka.

Wata sanarwa da ɓangaren hulɗa da jama’a na IRGC ya fitar ranar Litinin ta ce atisayen mai taken “Smart Control of the Strait of Hormuz” an yi shi ne domin tabbatar da shirin dakarun ruwanta.

Ta ce an yi atisayen ne domin tantance shirin tsaro da kuma yanayi na ramuwar gayya na matakin soji a matsayin martani ga barazanar soji a yankin mashigin tekun Hormuz da kuma nuna ƙarfin faɗa-a-ji da Iran take da shi a siyasar yankin.

“Martani na gaggawa, cikakke kuma galaba ta dakaraun IRGC game da makirce-makirce kan tsaro a ɓangaren ruwa shi ne abin da waɗannan dakarun da ke wannan atisayen suka mayar da hankali a kai,” in ji sanarwar.

Masu AlakaTRT Afrika - Iran ba za ta amince da bukatu barkatai ba - Shugaba Pezeshkian

Mashigin tekun Hormuz, ɗaya daga cikin tsukakkun wurare mafi muhimmanci a duniya da ke tsakiyar mashigin ruwan Oman kuma yana samar da hanyar ruwa ɗaya tilo daga mashigin tekun zuwa cikin teku.

Atisayen na zuwa ne a cikin yanayi na ƙarin ce-ce-ku-ce tsakanin Tehran da Washington, bayan jibge jiragen ruwa masu ɗauke da jiragen yaƙi da jiragen kai hare-haren bam a mashigin tekun Iran

Ranar Juma’a, shugaban Amurka Donald Trump ya ce za a tura wani jirgin ruwa mai ɗauke da jiragen yaƙi zuwa gabas ta Tsakiya.

Rumbun Labarai
Iran ba za ta amince da bukatu barkatai ba - Shugaba Pezeshkian
Trump ya yi barazanar ɗaukar 'mataki mai tsanani' kan Iran yayin da Netanyahu ya tafi Washington
Fidan na Turkiyya ya ce amfani da hare-haren sama ba zai rushe gwamnatin Iran ba
Shugaban Iran Pezeshkian ya bayyana tattaunawar nukiliya da Amurka a matsayin 'ci gaba' ga Tehran
Turkiyya da Saudiyya sun jaddada goyon bayansu ga haɗin kan Somaliya da zaman lafiyar yankin
Khamenei ya yi gargaɗi kan yaƙin yanki idan Amurka ta kai hari kan Iran
Iran ta ayyana rundunonin sojin ƙasashen Turai a matsayin 'ƙungiyoyin ta'addanci'
A 'shirye' Iran take don 'yarjejeniyar nukiliya ta gaskiya da adalci': Ministan Harkokin Wajen Iran
Waɗanne abubuwa ne za su iya faruwa idan Amurka ta kai hari Iran?
Iran ta ce duk maƙociyar da ta bari aka yi amfani da ita wurin kai mata hari 'abokiyar gaba' ce
Isra'ila na karya yarjejeniyar tsagaita wuta a Lebanon, ta ci gaba da kai hari
Manyan jami'an China sun tattauna da Ƙungiyar OIC a yanayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke ƙara muni
Yaƙin da ake yi da ta'addancin Daesh yana ƙara ƙarfi: Erdogan
Iran ta gargaɗi Amurka: 'Za mu ɗauki kowane irin hari a matsayin cikakken yaƙi a kanmu'
Turkiyya ba ta goyon bayan tsoma bakin ƙasashe waje a kan Iran – Erdogan
Adadin mutanen da suka mutu a zanga-zangar Iran ya kai  4,000: Rahoto
Syria ta cim ma tsagaita wuta don karɓe iko da arewa maso gabas daga hannun ‘yan ta’addan YPG
Iran ta sha alwashin gwabza yaƙi da duk ƙasar da ta yi gangancin kai wa Khamenei hari
Syria ta ayyana harshen Kurdanci a matsayin 'harshen ƙasa', sannan ta ba Kurdawa haƙƙin 'yan ƙasa
An buɗe sararin samaniyar Iran bayan rufe shi na wucin-gadi