| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Amurka ta aika kayayyakin soji ga Nijeriya bayan ƙaddamar da ayyukan tsaro na haɗin gwiwa
Aika kayan ya biyo bayan hare-haren sama da Amurka ta kai a ranar Kirsimeti a arewa maso yammacin Nijeriya.
Amurka ta aika kayayyakin soji ga Nijeriya bayan ƙaddamar da ayyukan tsaro na haɗin gwiwa
Amurka ta aika kayayyakin soji ga Nijeriya bayan ƙaddamar da ayyukan tsaro na haɗin gwiwa
13 Janairu 2026

Amurka ta kai muhimman kayayyakin soji ga Nijeriya don tallafa wa ayyukan tsaro da kasar ke gudanarwa, wanda hakan ke karfafa dangantakar tsaro tsakanin kasashen biyu.

A cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin X, rundunar sojin Amurka ta Afirka (AFRICOM) ta ce sojojin Amurka sun kai kayayyakin ga abokan huldarta Nijeriya a Abuja, inda ta lura cewa isar da kayayyakin yana goyon bayan kokarin sojojin Nijeriya na yanzu kuma yana nuna muradun tsaro iri daya.

Ofishin jakadancin Amurka a Nijeriya shi ma ya amince da isar da kayayyakin.

Aika kayan ya biyo bayan hare-haren sama da Amurka ta kai a ranar Kirsimeti a arewa maso yammacin Nijeriya.

A ranar 25 ga Disamban 2025, sojojin Amurka sun kai hari kan wurare a jihar Sokoto a wani abu da hukumomin Nijeriya suka bayyana a matsayin wani aiki na hadin gwiwa da kai hari kan 'yan bindiga da ke da alaka da kungiyar IS.

Hare-haren sun nuna babban ci gaba a hadin gwiwar tsaro tsakanin Amurka da Nijeriya, in ji ƙasashen.

Masu AlakaTRT Afrika - Trump ya yi barazanar kai ƙarin hare-hare a Nijeriya

Harin bama-baman Amurkan a Nijeriya na watan Disamba ya zo ne bayan wani lokaci na rashin jituwa tsakanin Washington da Abuja.

Dangantaka ta taɓarɓare a karshen shekarar da ta gabata lokacin da Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana rashin tsaron da ake fama da shi a Nijeriya a matsayin "tsanantawa" da yi wa "Kiristoci kisan kare dangi" - wani abu da gwamnatin Nijeriya da masu sharhi masu zaman kansu suka ƙi amincewa da shi.

Nijeriya, kasa mafi yawan jama'a a Afirka, tana fuskantar kalubalen tsaro da dama, ciki har da rikicin Boko Haram tun 2009, da masu fashi da makami, da sauran ayyukan laifuka masu dauke da makamai, musamman a arewacin ƙasar.

Kwanaki kafin harin Amurka, Ministan Yada Labarai na Nijeriya ya ce an warware "rikicin" diflomasiyya da Washington, wanda ya haifar da karfafa kawance tsakanin kasashen biyu. Wata majiya daga Nijeriya da ta saba da shirye-shiryen tsaro bayan harin ta shaida wa AFP cewa Rundunar Sojan Sama ta Nijeriya za ta jagoranci ayyukan da za a yi nan gaba, tare da Amurka ta ba da tallafin leken asiri ta hanyar jiragen leken asiri.

Rumbun Labarai
Jan hankalin gwamnatin Nijeriya ga 'yan ƙasar masu shiga yaƙi a wasu ƙasashen ƙetare
Rundunar Sojin Nijeriya ta ce ta daƙile hare-haren 'yan ta'adda a jihar Borno
Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar kan faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata su tura su wurin yaƙi
'Yanbindiga sun kashe aƙalla mutum 30 a Jihar Neja ta Nijeriya, sun ƙona ofishin 'yansanda
'Yanbindiga sun kashe DPO na 'yansandan Nijeriya a Jihar Katsina
'Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa'
Za a yi zaben Shugaban Kasa a Nijeriya ranar 20 ga Fabrairun 2027, in ji INEC
Hukumar Kiyaye Haɗɗura ta Nijeriya ta kori ma'aikatanta 43 kan saɓa wa dokar aiki
Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi
Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno
CBN ya bai wa 'yan canji a Nijeriya damar sayen dala 150,000 a duk mako daga gwamnati
Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun kashe gomman 'yan-ta'adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas
Me ya sa Kannywood ke fafutuka yayin da Nollywood ke samun tagomashi?
Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa
Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano
Nijeriya: 'Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku
Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan jigilar kayayyaki da tsaron kan iyaka
Shugaba Tinubu na Nijeriya na shirin kai ziyarar aiki London a watan Maris
Jerin hare-hare sun yi sanadin mutuwar mutum 30 a Jihar Benue ta Nijeriya