Dalibai tara da ake zargi da tayar da gobara wadda ta yi sanadiyar mutuwar 'yan mata 16 a wata makaranta da ke tsakiyar Kenya sun gurfana a gaban kotu ranar Talata.
Masu bincike sun nemi a ƙara musu lokaci don bincika ken musabbabin mummunar gobarar.
Kotun Koli da ke garin Naivasha, mai nisan kilomita 90 (mil 55) yamma da babban birnin Nairobi, ta ce za ta yanke hukunci a ranar Laraba kan ko za a iya tsare 'yan matan na tsawon wata guda yayin da ake kan bincike.
Gobarar da ta faru a ranar 28 ga Mayu ta ratsa ɗakin kwanan dalibai na Kwalejin 'Yan Mata ta Utumishi wanda ke ɗauke da ɗalibai 202. Matron ɗin makarantar ta kasa buɗe ƙofar da wuri, lamarin da ya tilasta wa ɗaliban su nemi mafita wajen tsarewa ta ƙofa ɗaya, a cewar masu bincike.
Cinna wa katifa wuta
'Yanmatan da ake zargin da aikata wannan mummunan aiki sun shafe kwana biyar a hannun 'yan sanda, a lokacin da aka yi musu tambayoyi, an gano cewa gobarar ta tashi ne sakamokon cinna wuta kan katifar da ke bakin ƙofar ɗakin kwanan daliban ta amfani da ashana da karanzir. Ko da yake ba a bayyana wani dalili da haifar da hakan ba zuwa yanzu.
Ana sa ran samun sakamakon gwajin DNA don gano asalin wasu gawarwakin da suka ƙone da ba za iya tantance su a ranar Laraba.
Hotunan na’urar CCTV da aka samu daga ɗakin kwanan daliban sun nuna ɗalibai shida suna kunna wutar jim kaɗan kafin sauran ɗaliban su farka, kana sun gaggauta tserewa daga gobarar wadda ta yi sanadiyyar jikkata mutane 79.
Tun bayan faruwar lamarin, an sake samun wasu ƙarin gobara a makarantu guda biyar a sassa daban-daban na ƙasar, kuma tun daga farkon shekarar nan hukumar Red Cross ta Kenya ta kai daukin gaggawa ga makarantu 37 da suka samu iftila’in gobara. Ba a samu asarar rai daga ko daga ko ɗaya daga cikin gobarar da aka samu.
Yawan gobara a makarantu
Ana yawan samun gobara a makarantu a Kenya, inda azuzuwa da ɗakunan kwanan dalibai galibi suke cike da jama'a kuma ba kasafai ake samun kayan aiki na kashe gobara ba.
Mafi munin lamarin da aka samu ya faru ne a shekarar 2001, lokacin da ɗalibai 67 suka mutu a gundumar Machakos, sai kuma wanda ya faru a shekarar 2024, lokacin da yara 21 suka mutu a gundumar Nyeri.
Kazalika an yi ta samun rahotannin cewa dalibai suna kona makarantu soboda ladabtar da su da ake yi.















