| Hausa
DUNIYA
3 minti karatu
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
Ficewar ta fara aiki daga 22 ga Janairun 2026, bayan an bi sharadin sanarwa na shekara guda bisa dokokin kasa da kasa.
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78
WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78 / Reuters
23 Janairu 2026

Amurka ta kammala ficewa daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) a hukumance, inda ta kawo karshen kusan shekaru 78 na kasancewa mamba a wannan hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya, in ji jami'an Amurka.

Ficewar ta fara aiki daga 22 ga Janairun 2026, bayan an bi sharadin sanarwa na shekara guda bisa dokokin kasa da kasa.

Sakataren Harkokin Waje Marco Rubio da Sakataren Lafiya da Ayyukan Jama'a Robert F. Kennedy Jr. sun sanar da wannan mataki, suna cewa Amurka ta fice daga WHO kuma ta sake 'yantar da kanta daga takunkumin ƙungiyar.

Jami'an sun ambaci abin da suka bayyana a matsayin gazawar WHO a lokacin annobar COVID-19, ciki har da yadda ta gudanar da ayyukanta a lokacin barkewar cutar da ta fara a Wuhan, China.

Sun zargi hukumar da ɗaukar ajanda ta siyasa da ta ma'aikata, hana musayar bayanai cikin lokaci da kuma yin aiki wanda ya saba wa muradun Amurka a ƙarƙashin tasirin ƙasashen da ke adawa da ita.

Sun ce haɗin gwiwar Amurka da WHO yanzu za a iyakance shi ne kawai ga aiwatar da tsarin ficewa da kuma tabbatar da lafiyar da tsaron rayukan 'yan Amurka.

A cewar sanarwar, an dakatar da dukkan tallafin kudi da ma'aikata na Amurka da ke kan ayyukan WHO.

Jami'an sun ce an dawo da ma'aikatan Amurka, kuma kasar ta mayar da hankali kan hada kai tsakaninta da kasashe abokan huldarta kawai kai-tsaye da kuma hanyoyin da ba su da alaka da juna don kokarin kiwon lafiya na duniya.

Daraktan Janar na WHO, Dr Tedros Adhanom Ghebreyesus, sau da yawa ya nuna bakin ciki kan wannan mataki, yana kwatanta ficewar a matsayin abun da babu wanda ya ci nasara kuma yana cewa ba ita ce shawara mai kyau ba.

An kafa WHO a ranar 7 ga Afrilun 1948. Amurka ta kasance ɗaya daga cikin masu sanya hannu na asali kan kundin tsarinta a 1946 kuma ta rattaɓa shi a hukumance a Yuni 1948, inda ta zama babbar mamba ta kafa hukumar.

Shugaba Trump ya daɗe yana sukar WHO sosai, musamman a lokacin annobar COVID-19 da bayanta. Ya zargi ƙungiyar da rashin kyakkyawan tafiyar da matakan farko na barkewar cutar, saboda alaƙarta ta ƙut da ƙut da China, da maimaita bayanan da ba daidai daga Beijing da kuma siyasaƙe rikicin ta hanyar kiran haramcin tafiye-tafiye na Amurka daga China a matsayin rashin adalci.

Trump ya kuma soki abin da ya bayyana a matsayin ɗora wa Amurka nauyin kashe kuɗaɗe na rashin adalci, yana cewa ita ke biyan kuɗaɗe masu yawa fiye da sauran ƙasashe, ciki har da China, ba tare da samun kyakkyawar mu'amala a matsayin riba ba.

A lokacin wa'adin mulkinsa na biyu, Trump ya aiwatar da waɗannan suka ta hanyar fitar da Amurka daga WHO a 2025, wanda ya kawo ƙarshen zamanta mamba da tallafin Amurka bayan kusan shekaru tamanin.

Rumbun Labarai
An ci tarar ƙananan hukumomi 10 a Holland kan binciken al'ummomin Musulmai ba tare da saninsu ba
Trevor Noah: Trump ya yi barazanar maka mai gabatarwa a Gasar Grammy a Kotu
Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu 'mai shekara 67,800' a wani kogo a Indonesia
Ministan Wajen Saudiyya da takwarorinsa na Iran, Oman da Qatar sun tattauna kan zaman lafiyar yanki
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga 'yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa
Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran
An katse intanet da wayoyin hannu a Iran
Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara
Sanatocin Republican 5 sun bi sahun 'yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Erdogan da Anwar na son ƙarfafa alaƙar Turkiyya da Malaysia tare da fifita fannin tsaro
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Abin da ya sa ya kamata Afirka ta damu kan samamen da Amurka ta kai Venezuela
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
Me zai faru ga takunkuman da Amurka ta sanya wa Venezuela bayan ta ɗauke Maduro
Tarayyar Afirka ta nuna 'damuwa', Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro