| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a Jihar Benue da ke tsakiyar Nijeriya, in ji mazauna yankin
'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a jihar Binuwe ta arewa matso tsakiyar Nijeriya a hare-haren da suka kai a ƙarshen makon jiya, kamar yadda mazauna yankin da jami'ai suka bayyana.
'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a Jihar Benue da ke tsakiyar Nijeriya, in ji mazauna yankin
'Yan bindiga sun kashe aƙalla mutane 18 a jihar Benue da ke arewacin Najeriya a ranar 12 ga watan Yuli, 2026.

'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a jihar Binuwe ta arewa maso tsakiyar Nijeriya a harin da aka kai a ƙarshen mako, in ji mazauna da jami'an yankin.

Mai magana da yawun 'yansanda a Jihar, Udeme Edet, ya bayar da ƙididdiga mafi ƙaraanci ta adadin mutanen da suka mutu a harin da ya faru da safe a ranar Lahadi, yana cewa mutum takwas sun mutu sannan biyar sun ji raunuka.

Sai dai wasu jaridun Nijeriya sun ce adadin waɗanda aka kashe ya kai 18 a hare-haren da aka fara kaiwa tun ranar Juma’a.

Lamarin na baya-bayan nan ya faru ne a al'ummar Otukpo-Nobi a ƙaramar hukumar Otukpo, inda mazauna suka ce wasu mutane ɗauke da makamai sun buɗe wuta tsakanin da misalin ƙarfe 3:30 da 4:30 na asuba.

Shugaban ƙaramar hukuma Maxwell Ogiri ya danganta tashin hankalin da aka gani da kisan shugaban ƙungiyar makiyaya Fulani da aka yi makonni biyu da suka wuce.

Sai dai Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah MACBAN reshen Jihar ta Binuwe ta nesanta kanta da kashe-kashen, sannan ta yi Allah wadai da hare-haren, kamar yadda ke ƙunshe a wata sanarwa da sakataren ƙungiyar Ibrahim Galma ya sanya wa hannu.

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin harin.

Mata da matasa daga yankin da abin ya shafa sun yi zanga-zanga a garin Otukpo don nuna adawa da kisan.

Rumbun Labarai
‘Yansandan Nijeriya 10 sun rasa rayukansu a musayar wuta da mahara a arewacin ƙasar, in ji hukumomi
'Yan Nijeriya sun kashe Naira tiriliyan 6.6 kan sayen datar waya a cikin shekara ɗaya
Mutane 237 ne suka mutu sakamakon zazzaɓin Lassa a watanni bakwai na 2026 a Nijeriya - NCDC
Sojojin Nijeriya sun kashe Abu Khalid Al Muhajir da wasu  kwamandojin ISWAP tara a Borno
Masarautar Kano ta musanta bidiyon da ake yadawa kan Sarki Sanusi II ya samu 'carry-over' a jami'a
Super Falcons da Indomitable Lionesses na gogayyar shiga Gasar Kofin Duniya
Gwamnatin Nijeriya za ta fara sarrafa kayayyakin tsara iyali a cikin ƙasar
Hukumar EFCC ta rufe asusun gwamnatin Jihar Osun kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamna
Rundunar sojin Nijeriya ta sanya tukuicin N60m kan kwamandan ISWAP da mataimakinsa
An yi motsin ƙasa a wasu sassan Abuja
An saki gomman mutanen da aka yi garkuwa da su a Jihar Kwara bayan wata shida a hannun ‘yanta'adda
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa  'yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
An saki alƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun daƙile harin daren 'yanta'adda kan sansanin soji
'Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauye Sokoto a Nijeriya
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau
Sojojin Nijeriya sun daƙile yunƙurin 'yanta'adda na garkuwa  da mutane 31 a Borno