| Hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a Jihar Benue da ke tsakiyar Nijeriya, in ji mazauna yankin
'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a jihar Binuwe ta arewa matso tsakiyar Nijeriya a hare-haren da suka kai a ƙarshen makon jiya, kamar yadda mazauna yankin da jami'ai suka bayyana.
'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a Jihar Benue da ke tsakiyar Nijeriya, in ji mazauna yankin
'Yan bindiga sun kashe aƙalla mutane 18 a jihar Benue da ke arewacin Najeriya a ranar 12 ga watan Yuli, 2026.

'Yanbindiga sun kashe mutane aƙalla 18 a jihar Binuwe ta arewa maso tsakiyar Nijeriya a harin da aka kai a ƙarshen mako, in ji mazauna da jami'an yankin.

Mai magana da yawun 'yansanda a Jihar, Udeme Edet, ya bayar da ƙididdiga mafi ƙaraanci ta adadin mutanen da suka mutu a harin da ya faru da safe a ranar Lahadi, yana cewa mutum takwas sun mutu sannan biyar sun ji raunuka.

Sai dai wasu jaridun Nijeriya sun ce adadin waɗanda aka kashe ya kai 18 a hare-haren da aka fara kaiwa tun ranar Juma’a.

Lamarin na baya-bayan nan ya faru ne a al'ummar Otukpo-Nobi a ƙaramar hukumar Otukpo, inda mazauna suka ce wasu mutane ɗauke da makamai sun buɗe wuta tsakanin da misalin ƙarfe 3:30 da 4:30 na asuba.

Shugaban ƙaramar hukuma Maxwell Ogiri ya danganta tashin hankalin da aka gani da kisan shugaban ƙungiyar makiyaya Fulani da aka yi makonni biyu da suka wuce.

Sai dai Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah MACBAN reshen Jihar ta Binuwe ta nesanta kanta da kashe-kashen, sannan ta yi Allah wadai da hare-haren, kamar yadda ke ƙunshe a wata sanarwa da sakataren ƙungiyar Ibrahim Galma ya sanya wa hannu.

Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin harin.

Mata da matasa daga yankin da abin ya shafa sun yi zanga-zanga a garin Otukpo don nuna adawa da kisan.

Rumbun Labarai
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa  'yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
'Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
An saki alƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
Dakarun Nijeriya sun daƙile harin daren 'yanta'adda kan sansanin soji
'Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauye Sokoto a Nijeriya
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau
Sojojin Nijeriya sun daƙile yunƙurin 'yanta'adda na garkuwa  da mutane 31 a Borno
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Nijeriya ta lalata makamai guda 2,819 da ta kama a matakin dakile rashin tsaro
'Yansandan InterPol sun tasa ƙeyar ɗan China daga Nijeriya kan safarar namun daji
Nijeriya na da attajirai 7,200 masu arzikin dala miliyan 1 duk da raguwar kuɗi - Rahoto
'Yanbindiga sun kashe Kanar na sojin Nijeriya bayan ya ƙi amincewa su yi garkuwa da shi
Aƙalla mutane 14 ne suka mutu a wani hari da aka kai a jihar Benue ta Nijeriya, in ji jami’an yankin
'Yanta'adda sun kashe aƙalla mutum 30 a wani ƙauye a Kaduna ta Nijeriya
Ana fargabar ɗalibai sun maƙale bayan da gini mai ɗakuna 90 ya rufta da su
Rundunar Sojin Nijeriya ta kama jami'in da ake zargi da sayar wa 'yanta'adda kayan soji
Jami'in da ke kula da harkokin kuɗin ISWAP ya miƙa wuya —Rundunar Sojin Nijeriya
INEC za ta rufe rijistar masu zaɓe ranar Lahadi, 'yan adawa na neman a tsawaita lokacin rijistar