| Hausa
GABAS TA TSAKIYA
3 minti karatu
Saudiyya ta kai hare-haren sirri kan Iran bayan an kai mata hari — Rahoto
Rahoton ya ce waɗannan hare-hare na Saudiyya, da ba a taɓa bayyana su a baya ba, su ne karon farko da aka tabbatar cewa masarautar ta kai farmaki kai tsaye a ƙasar Iran.
Saudiyya ta kai hare-haren sirri kan Iran bayan an kai mata hari — Rahoto
Wani jirgin yaƙin Saudiyya ya raka Air Force One, jirgin shugaban Amurka Donald Trump, yayin da yake kusantar filin jirgin sama na Riyadh, a Saudiyya. / Reuters

Rahoto ya bayyana cewa Saudiyya ta kai wasu hare-hare da dama a ɓoye kan Iran a matsayin ramuwar gayya ga hare-haren da aka kai mata a cikin masarautar yayin yakin Gabas ta Tsakiya, kamar yadda wasu jami’an yammacin duniya biyu da kuma jami’an Iran biyu suka shaida.

Rahoton ya ce waɗannan hare-hare na Saudiyya, da ba a taɓa bayyana su a baya ba, su ne karon farko da aka tabbatar cewa masarautar ta kai farmaki kai tsaye a ƙasar Iran.

Wannan kuma ya nuna cewa Riyadh na ƙara ƙarfafa matsayinta wajen kare kanta daga babbar abokin hamayyarta a yankin.

Jami’an sun ce an kai harin ne da jiragen yaƙi na sojin saman Saudiyya a ƙarshen watan Maris, inda ɗaya daga cikinsu ya bayyana cewa “ramuwar gayya ce bisa hare-haren da aka kai wa Saudiyya.”

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce bai samu tabbacin takamaiman wuraren da aka kai harin ba.

A martanin da ya bayar, wani babban jami’in ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya bai tabbatar ko ya musanta faruwar hare-haren ba. Haka kuma ma’aikatar harkokin wajen Iran ba ta mayar da martani ba kan bukatar jin ta.

Rahoton ya ce Saudiyya, wadda ke da alaƙar soja mai ƙarfi da Amurka, ta dade tana dogaro da kariyar sojojin Amurka, amma yakin da ya ɗauki makonni 10 ya bar masarautar cikin yanayin rauni, inda kariyar Amurkar bai hana kai mata hare-hare ba.

Kasashen Gulf sun fara mayar da martani

Rahoton ya nuna cewa wannan rikici na kara faɗaɗa, inda yakin da ya fara bayan hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai Iran a ranar 28 ga Fabrairu ya jawo sauran ƙasashen Gabas ta Tsakiya cikin rikicin ta hanyoyin da ba a bayyana a fili ba.

Tun bayan wadannan hare-hare, Iran ta kai hare-hare da makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa kan dukkan ƙasashen Hadaddiyar Ƙungiyar Kasashen Gulf (GCC), inda ta kai hari ba kawai sansanonin sojojin Amurka ba, har ma da wuraren fararen-hula, filayen jirgin sama da cibiyoyin mai, tare da rufe Mashigar Ruwan Hormuz wanda ke shafar kasuwancin duniya.

Rahoton ya kuma ce Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ita ma ta kai hare-haren soja kan Iran, kamar yadda jaridar Wall Street Journal ta ruwaito.

Wannan ya nuna cewa ƙasashen Gulf sun fara mayar da martani a ɓoye kan Iran bayan hare-harenta.

Sai dai rahoton ya ce dabarun ƙasashen biyu sun bambanta, inda UAE ke nuna matsaya mai tsauri wajen mayar da martani, yayin da Saudiyya ke ƙoƙarin rage tashin hankali tare da ci gaba da tattaunawa da Iran.

Wani jami’in ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya ya ce masarautar na ci gaba da matsayarta na neman zaman lafiya da rage tashin hankali domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a yankin.

Rumbun Labarai
Iran ta ce ta kai hari kan wani jirgi mai alaƙa da Amurka da Isra'ila bayan hari kan wani jirginta
Iran ta dakatar da tattaunawa da Amurka saboda hare-haren Isra'ila a Lebanon: rahoto
Iran ta kai hari sansanin sojin Amurka a Kuwait bayan hari kan benen sadarwar Hormozgan
Masar ta yi kira ga kwamitin tsaro na MƊD ta dakatar da faɗaɗa [harin] da Isra'ila ke yi a Lebanon
Iran ta ci gaba da aikin samar da gas a wurarenta uku na South Pars da ke cikin teku
Netanyahu ya kira taron gaggawa bayan Hezbollah ta kai hari na ban mamaki ga sojin Isra'ila
Zaman jiragen sojojin Amurka ya janyo wa filin jirgin saman Ben Gurion na Israila asarar $248M
Dakarun Juyin-Juya-Hali na Iran sun ce sun kai hari sansanin Amurka na sama a Kuwait
Amurka ta kai sabbin hare-hare a wuraren soji a kudancin Iran — rahoto
Rundunar sojin Isra'ila ta yi ikirarin kashe shugaban rundunar sojin Hamas a wani babban hari a Gaza
Musulmai sun yi sallar idin Babbar Sallah a Masallacin Ƙudus a Gabashin Birnin Ƙudus da aka mamaye
Iran ta yi iƙirarin harbo jirgin yaki mara matuƙi na Amurka tare da tilasta wa wasu ja da baya
Sojojin Amurka sun kai hari kan jiragen yaƙi na ruwa da wuraren makamai masu linzami a kudancin Iran
Ƙasashe 10 sun gayyaci jakadun Isra’ila kan bidiyon cin zarafin da Ben-Gvir ya yi wa ayarin Sumud
Hezbollah ta ce ta kai hare-hare 24 kan dakarun mamaya na Isra'ila a kudancin Lebanon cikin sa'a 24
Iran ta yi gargaɗin cewa sabon harin Amurka da Isra'ila zai iya faɗaɗa rikici fiye da yankin
Amurka za ta kawo ƙarshen yaƙi da Iran 'cikin gaggawa', a cewar Trump
Iran ta bayyana cikakkun bayanai na shawarwari 14 ga Amurka da nufin kawo ƙarshen yaƙi
'Lokaci na ƙurewa' Trump ya yi gargaɗi ga Iran yayin da ƙofofin diflomasiyya ke rufewa
Saudiyya ta ce an tare jirage uku marasa matuƙa bayan sun shiga sararin samaniyar ƙasar daga Iraq