Gwamnatin Trump na shirin tasa ƙeyar wasu ‘yan Iran da wasu baƙi zuwa Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya, kamar yadda lauyoyi biyu da wani jami’i suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
‘Yan Iran ɗin sun haɗa da mata biyu, kamar yadda lauyarsu , Emily Trostle, ta bayyana.
Matan biyu sun nemi mafaka a Amurka kuma sun sami wani nau’i na kariya da ake cewa hana fitarwa, a cewar Trostle.
Jami’in da aka yi wa bayani kan lamarin ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewar jirgi na farko zai tashi zuwa Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya a ƙarƙashin wata yarjejeniya da ake tsammanin za ta ɗauki kimanin mutum 20, waɗanda suka haɗa da ‘yan Syria da ‘yan Afghanistan. Jirgin zai iya tashi daga ranar Alhamis, in ji lauyoyin.
Iran ta kai hari
Gwamnatin Trump ta yi amfani da yarjejeniyar tasa ƙeyar baƙi zuwa ƙasashen da ba daga nan suka fito ba idan ba za ta iya mayar da su gida ba. Washington ta kare yarjejeniyoyin a matsayin wani abu da ta dace yana kan doka.
Amurka da Isra’ila sun ƙaddamar da hare-hare na haɗin gwiwa kan Iran a ƙarshen watan Fabrairu, lamarin da ya haifar da yaƙin da a yanzu aka kai wata uku ana yi.
Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da manema labarai a watan Afrilu cewa ya yi tunanin cewa ya kamata a ‘yan Iran su yi wa gwamnati bore idan an ayyana yarjejeniyar tsagaita wuta, amma ya gane cewa yin hakan na da hatsari sosai.
Waɗanda aka tasa ƙeyarsu za a ajiye su a babban birnin ƙasar Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya kuma ba a tsammanin za a mayar da su ƙasashensu nan take, kamar yadda jami’in da aka yi wa bayani ya bayyana. Za a iya tasa ƙeyar ɗaruruwan baƙi wurin a ƙarƙashin yarjejeniyar, kamar yadda jami’in ya bayyana.
IOM ta ce ba da hannu a yarjejeniyar CAR
Daga farkon a ranar Alhamis ne jaridar The New York Times ta ba da rahoton shirin na tasa ƙeyar Iraniyawan.
Ma’aikatar tsaron cikin gida ta Amurka ta bayyana a makon da ya gabata cewa dukkan waɗanda za a tasa ƙeyarsu za su samu cikakkiyar dama ta hanyar bin sharruɗan da suka kamata.
Wani mai magana da yawun Hukumar da ke Kula da Ƙaura ta Duniya (IOM) ya ce hukumar za ta "ba da taimako na jinƙai bayan baƙin sun isa Bangui, bisa buƙatar gwamnatin Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya.
Ya ce IOM ba ta da hannu a shirin fitar da mutanen daga Amurka kuma za ta ba da taimako "bisa sa-kai ne kawai da kuma mutunta ƙa’idoji na ƙasa da ƙasa."
A bana, Amurka ta bai wa IOM dala miliyan $85 domin ayyuka a Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya, wadda ke da yawan jama’a miliyan 5.5.













