| Hausa
AFIRKA
2 minti karatu
Shugaban Guinea Doumbouya ya yi alkawarin ba zai yi amfani da ofishinsa don biyan buƙatar kansa ba
An rantsar da Doumbouya a hukumance a ranar Asabar a matsayin shugaban Jamhuriyar Guinea bayan ya lashe zaben shugaban ƙasa na 28 ga Disamba da kashi 86.72 cikin 100 na kuri'u
Shugaban Guinea Doumbouya ya yi alkawarin ba zai yi amfani da ofishinsa don biyan buƙatar kansa ba
Doumbouya, jagoranci Guinea tun Satumban 2021, lokacin da ya karɓi iko a juyin mulkin soja da ya kifar da tsohon shugaban ƙasa Alpha Condé. / Reuters
18 Janairu 2026

Shugaban Guinea da aka rantsar kwanan nan, Mamadi Doumbouya, ya yi alkawarin ba za ya yi amfani da ikonsa na shugaban kasa don amfanar da kansa ba; inda ya ce 'ba zai taɓa amfani da ikon da aka ba shi don bukatun kansa ba'.

An rantsar da Doumbouya a hukumance a ranar Asabar a matsayin shugaban Jamhuriyar Guinea bayan ya lashe zaben shugaban ƙasa na 28 ga Disamba da kashi 86.72 cikin 100 na kuri'u, alamar dawowar ƙasar ga mulkin farar-hula bayan fiye da shekaru huɗu na mulkin soja.

Bikin rantsuwar ya gudana a Filin Wasa na Janar Lansana Conté a Nongo, da ke gefen birnin Conakry, tare da halartar shugabanni da dama na Afirka da manyan wakilai daga sassa daban-daban na duniya. Doumbouya zai yi wa'adin shekaru bakwai.

Shugabannin Afirka a bikin rantsuwa

Kamar yadda Sahe na 59 na Kundin Tsarin Mulkin Guinea ya tanada, Doumbouya ya yi rantsuwa gaban Kotun Kolin, wadda shugaban ta na farko Fode Bangoura ya jagoranta, ya yi alkawarin biyayya ga ƙasa da girmama doka.

Shugaban Rwanda Paul Kagame, Shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye, Shugaban Mali Assimi Goita, Shugaban Gambia Adama Barrow, Shugaban Mauritaniya Mohamed Ould Ghazouani, Shugaban Gabon Brice Oligui Nguema, Shugaban Saliyo Maada Bio da Shugaban Liberia Joseph Boakai na daga cikin shugabannin Afirka da suka halarci bikin rantsuwar.

An rufe babin mulkin soja

Mataimakan shugabannin kasashe daga China, Nijeriya, Ghana da Equatorial Guinea sun halarci bikin ranstuwar, tare da manyan 'yan majalisa da jami'an gwamnati daga Côte d’Ivoire, Maroko, Togo, Guinea-Bissau da Tarayyar Komoros.

Shugabannin Kwamitin ECOWAS da Kwamitin Hukumar Tarayyar Afirka ma sun halarci taron.

Rantsuwar ranar Asabar ta tabbatar da sauyawar Doumbouya daga shugaba na soja zuwa shugaban farar-hula da aka zaba. Ya jagoranci Guinea tun Satumban 2021, lokacin da ya karɓi iko a juyin mulkin soja da ya kifar da tsohon shugaban ƙasa Alpha Condé.

An yi tsammanin canjin zai kasance na ɗan lokaci, amma ya ɗauki fiye da shekaru huɗu yayin tattaunawa da ƙungiyoyi na yankin, ciki har da Ƙungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS), wadda ta kakaba takunkumi a lokuta daban-daban don matsa lamba wajen samun jadawalin zaɓen dimokuradiyya.

An gudanar da zaɓen na 28 ga Disamban 2025, a matsayin mataki na ƙarshe wajen mayar da ƙasar a kan mulkin dimokuradiyya.

Rumbun Labarai
Afirka ce kan-gaba wajen faɗaɗa samar da lantarki ta hasken rana a shekarar 2025: Rahoto
Gwamnatin Ghana ta ba da umarnin sarrafa kashi 50 cikin 100 na koko a cikin ƙasar
Sudan: Aƙalla mutum 21 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kogin Nilu
Kasashe shida sun shiga Kwamitin Tsaro na Tarayyar Afirka
RSF ta kashe ƙananan yara a harin da ta kai wani masallaci a yankin Kordofan na Sudan
Saudiyya ta yi tur da RSF kan munanan ayyukanta a Al Fasher, ta buƙaci a ba da hanyar kai agaji
Mutum biyar sun mutu a hatsarin helikwaftan ɗaukar marasa lafiya a Libya
Yadda 'yan Somaliya suka gina wa tsohon shugaba ƙasarsu Farmaajo sabon gida
Sake dawo da ainihin martabar Afirka
RSF ta Sudan ta kai hari da jirgi maras matuƙi, ta kashe gomman mutane da yara
Dubban ‘yan kasar Libya sun taru don halartar jana'izar Saif al-Islam Gaddafi
Harin RSF a wani asibiti a Sudan ya kashe mutum 22, ciki har da ma'aikatan jinya
Ghana da Zambia sun ƙulla yarjejeniyar shiga ƙasashen juna ba tare da biza ba yayin ziyarar Mahama
Saif al-Islam Gaddafi: An kashe ɗan marigayi shugaban Libya Muammar Gaddafi
Afirka na fuskantar tarnaƙin bashin dala biliyan 90 a 2026, in ji S&P
Yadda Biteye na Senegal ke amfani da ƙwallon ƙafa don samun waraka ga ƙwaƙwalwa
Sojojin Rasha sun taimaka wajen daƙile hari a filin jirgin saman Nijar: Moscow
'Yanbindiga sun kashe sojojin Libya uku a kusa da kan iyakar Nijar
Sudan ta sake buɗe filin jiragen sama na Khartoum bayan yaƙin kusan shekaru uku
Nijar: Ƙungiyar Daesh ta ɗauki nauyin harin da aka kai sansanin sojin sama na Yamai