| Hausa
AFIRKA
3 minti karatu
Harin kare kan wata 'yar Afirka ta Kudu ya janyo kiraye-kirayen dokoki masu tsauri
Ana neman kare ɗaya yayin da aka kashe karnuka biyu cikin wani yanayi na tausayi.
Harin kare kan wata 'yar Afirka ta Kudu ya janyo kiraye-kirayen dokoki masu tsauri
Waɗanda ke wucewa sun yi yekuwa kuma sun yi ƙoƙarin taimaka, amma Kweleta ta mutu daga baya sakamakon raunin da ta ji

Ƙungiyar masu kiwon kare irin na Pit Bull na Afirka Ta Kudu (PBFSA) tana kira ga hukumomin gwamnati su ƙaddamar da dokokin tsaurara mallakar karnuka masu ƙarfi biyo bayan harin kisan da karnuka suka afka wa wata mai shekara 28 a Montclair, dake kudancin Durban.

Wadda lamarin ya shafa tana tafiya ne a kan hanyar gwamnati a lokacin da karnuka uku masu ƙarfi da ake ce wa pit bull suka afka mata kuma suka kashe ta. An binne ta ne a ƙarshen mako.

Kafafan watsa labaran ƙasar sun ruwaito cewa matar wadda aka bayyana cewa sunanata ne Nomathemba Kweleta tana kan hanyarta ta dawowa ne daga sayan kayan cefane a lokacin da karnukan suka kewata kuma suka far mata.

Waɗanda ke wucewa sun yi yekuwa kuma sun yi ƙoƙarin taimakawa, amma Kweleta ta mutu daga baya sakamakon raunin da ta ji.

Biyo bayan aukuwar lamarin, wani mai gadi ya harbe kare ɗaya kuma daga baya ya kashe shi cikin tausayi a wata cibiya ta hana cin zalin dabbobi.

An kama wani kare na biyu kusa da wurin daga wurin da lamarin ya auku kuma daga baya aka kashe shi cikin tausayi. Kare na ukun dai ana nemansa ruwa a jallo a lokacin rahoton.

Rahoton kafar SABC News ta ƙasar ta ba da rahoton cewa harin ya sake buɗe tattaunawa game da dokokin garuruwa da kuma nauyin da ya kamata masu karnuka suɗauka a lokacin da suka mallaki karnuka masu ƙarfi.

Rashin horaswa

Ƙungiyar PBFSA ta ce lammuran tsaro a bainar jama’a da ke da alaƙa da karnuka masu ƙarfi da rashin keɓe su da kiwonsu ba tare da ƙa’ida ba.

"Ƙarnuka masu ƙarfi, irin su, ba dabbobin gida irin ba na iyalai na yau da kullum ba ne," in ji ƙungiyar, tana mai jaddada cewa waɗannan dabbobin suna buƙatar sa-ido na msamman da kuma ƙwarewa wajen tafiyar da su.

A martani ga kiraye-kirayen da ake samu daga ƙungiyoyin masu fafatuka na neman haramta irin karnukan, in ji mai magana da yawun PBFSA Lehanda Rheeder wadda ta ce ya kamata a ɗabbaka dokar ta mayar da hankali kan fayyace gaskiya na masu karnukan da kuma bincike na doka maimakon haramtawa gaba ɗaya.

Rheeder ta ce "ya kamata a samu ƙa’ida mai tsauri game da waɗanda za su iya mallakar kare pit bull," tana mai kira ga sa-ido na garuruwa domin tantance ko waɗanda ke son mallakar karen suna da inda za su saka su da kuma horaswar da ta dace .

Rumbun Labarai
Mutane fiye da 4,000 ne suka kamu da cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo - Gwamnati
Kwamitin tattaunawa na Libiya ya cim ma matsaya kan tsarin ɗaukar shugaban hukumar zaɓe
Gargadin shugabannin Afirka kan cin abinci a makare da illolin shan siga da giya
Shugaba Biya na Kamaru ya yi sauye-sauye a shugabancin sojin ƙasar
Ghana ta amince da ɗaurin shekara 20 ga duk wanda ya mayar da gonar koko zuwa wani abu daban
Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren 'yanta'adda
‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati
Fitacciyar mawaƙiyar Afirka Ta Kudu ta soke kalankuwarta a Legas bayan an kori baƙi daga ƙasarta
Gwamnatin Ghana ta amince da shawara ƙara wa'adin mulkin shugaban ƙasa
Adadin 'yan ci-ranin da suka rasu ya kai 19 bayan dubbai sun tsallaka zuwa yankin Ceuta na Sifaniya
Biranen Afirka 25 da Amurka za ta rufe ayyukan bayar da biza daga ranar 1 ga Agustan 2026
Siyasar Kamaru: Ina Shugaba Paul Biya ya shiga?
Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 kan zargin ɓoye shi don haddasa ƙarancinsa
Hukumomin Libya a Benghazi sun kori baƙin-haure fiye da 117,000 daga ƙasar
Mutumin da ya fi kowa tsawo a Ghana Awuche ya rasu
Chadi ta sanar da shirin fita daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC)
An gudanar da zanga-zanga a Tripoli saboda tsadar rayuwa da tabarbarewar ayyukan gwamnati
Ƙarin ma'aikatan jinya sun shiga yajin aiki yayin da cutar Ebola ta kama kusan mutum 3,000
Yara na cikin waɗanda aka kashe a harin jirgi marar matuƙi a wata kasuwar Sudan
Jam'iyyar da ke mulki a Kamaru ta yi zama kan dogon hutun Shugaba Biya da ya jawo tambayoyi