| hausa
NIJERIYA
2 minti karatu
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
“Akwai ƙasashe da suke rayuwa waɗanda ba su san akwai wani abu Amurka ba, wannan ƙasar ba ta nuna mana tana ƙaunarmu ba, sai dai ta tatse manmu, ta raba mu, ta cutar da mu,” in ji fitaccen malamin.
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
Fitaccen malamin ya bayyana cewa Musulmai da Kirista suna zaune lafiya, babu ƙamshin gaskiya a kalaman Trump na Musulmi na kashe Kiristoci a Nijeriya.
10 Nuwamba 2025

Fitaccen Malamin Addinin Musuluncin nan na Nijeriya Sheikh Ahmad Mahmud Gumi ya bayyana cewa babu abin da Nijeriya za ta ragu da shi idan ta daina hulɗa da Amurka.

Ya bayyana haka ne a cikin ɓangaren wata hira da TRT Afrika Hausa ta yi da shi a daidai lokacin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Nijeriya na ɗaukar matakin soji a kanta.

“Ba Amurka ce kaɗai ƙasa a duniya ba da har za ka rasa wani abu idan ka daina hulɗa da ita, idan kayan ƙere-ƙere ne akwai China, idan kayan ƙarfi ne [makamai] akwai Rasha,” in ji Sheikh Gumi.

“Akwai ƙasashe da suke rayuwa waɗanda ba su san akwai wani abu Amurka ba, wannan ƙasar ba ta nuna mana tana ƙaunarmu ba, sai dai ta tatse manmu, ta raba mu, ta cutar da mu,” kamar yadda ya ƙara da cewa.

Sheikh Gumi ya jaddada cewa Amurka ba ta neman Nijeriya da alkhairi inda ya yi zargin cewa Amurkar na cikin waɗanda suka rinƙa taimaka wa yankin Biafra da ke son ɓallewa daga Nijeriya a lokacin yaƙin basasa.

Fitaccen malamin ya bayyana cewa Musulmai da Kirista suna zaune lafiya, babu ƙamshin gaskiya a kalaman Trump na Musulmi na kashe Kiristoci a Nijeriya.

 

Rumbun Labarai
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Damuwa kan kutsawar 'yan bindiga Jihar Kano
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
INEC ta ayyana Charles Soludo na APGA a matsayin wanda ya lashe zaɓen Gwamnan Anambra
Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi
‘Kisan kiyashi ga Kiristoci: Me ya sa kurarin Trump a Nijeriya yake kan kuskure da rashin dacewa?
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai
An kashe 'yan ta'adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 - Ministan Yada Labaran Nijeriya
ECOWAS ta yi tir da ikirarin ‘ƙarya mai hatsari’ na Amurka cewa Nijeriya ta bari ana kashe Kiristoci
Hukumar DSS a Nijeriya ta kori ma'aikatanta fiye da 100
Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da kisan Kiristoci - Sheik Bala Lau
China na adawa da Trump kan amfani da 'addini da ‘yancin ɗan'adam' domin tsoma baki a Nijeriya
Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar
Jami'an tsaron Nijeriya sun hallaka 'yan bindiga 19 a Jihar Kano
Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Ya kamata Amurka ta taimaka wa Nijeriya da makamai maimakon barazana —Kwankwaso
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya - Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka