| Hausa
SIYASA
2 minti karatu
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
Ministoci sun yi kira ga kwantar da hankali da neman sulhu don hana samun wasu jerin abubuwan ɗaga hankali a yankin.
Masar da Saudiyya sun yi kira ga samar da hanyoyin da suka dace kafin tattaunawar Amurka da Iran
An yi maganganun ne a wani taro a Riyadh tsakanin Ministan Harkokin Wajen Masar, Badr Abdelatty, da takwaransa na Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan. / Reuters
3 Fabrairu 2026

Ministocin harkokin wajen Masar da na Saudiyya sun yi kira da a bi hanyoyin diflomasiyya da kuma ƙirƙirar "yanayi mai kyau" don sake farfado da tattaunawa tsakanin Amurka da Iran domin cim ma yarjejeniya "mai fadi kuma mai daidaito".

Maganganun an yi su ne a yayin wata ganawa a Riyadh tsakanin Ministan Harkokin Wajen Masar, Badr Abdelatty, da takwaransa na Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan, a ranar Talata, in ji Ma'aikatar Harkokin Wajen Masar a cikin wata sanarwa.

Ministocin biyu sun kuma tattauna dangantaka tsakanin kasashen biyu yayin ganawar, inda suka nuna aniyarsu ta ƙarfafa tsarin haɗin gwiwa da ake da shi, in ji sanarwar.

Sun kuma jaddada muhimmancin ɗaukar matakan rage tashin hankali da hana barkewar rikici a yankin, "ta hanyar ƙara ƙoƙari don cim ma sassaucin zafi da fifita hanyoyin siyasa da diflomasiyya wajen warware rikice-rikice, don haka hana yankin shiga sabon zagayowar rashin daidaito."

"Ministocin biyu sun kuma tabbatar da cewa irin kalubalen da ake fuskanta a yankin na buƙatar haɗin kai na Larabawa da ci gaba da tuntuɓa da daidaita manufofi tsakanin kasashen Larabawa a matsayin ginshiƙi na asali wajen kare tsaron ƙasashen Larabawa a fuskar rikice-rikice na yanki," in ji ma'aikatar.

Haɗin gwiwa

"Abdelatty da bin Farhan sun jaddada muhimmancin aiwatar da alƙawuran mataki na biyu na tsarin Gaza na Shugaba Donald Trump na Amurka, goyon bayan Kwamitin Kasa don Gudanar da Gaza, tura ƙungiyar kwantar da tarzoma ta ƙasa da ƙasa cikin gaggawa, tabbatar da ci gaba marar katsewar shigar agajin ɗan’adam da kuma shimfiɗa tushe don farfadowa da sake ginawa."

Shugabannin diflomasiyyar sun kuma yi kira a ci gaba da haɗin gwiwa tare da ƙoƙarin samar da jinƙai na gaggawa a Sudan don buɗe hanya ga tsagaita wuta gabaɗaya da fara wani tsarin siyasa da 'yan Sudan za su mallaka gaba ɗaya.

Sun kuma jaddada buƙatar kiyaye haɗin kan Sudan, da tsaron ƙasar da iyakokinta, da kuma ƙarfafa hukumomin ƙasa.

Tun watan Afrilun 2023, Sudan tana cikin rikici da ake ta zubar da jini tsakanin rundunar soji da ƙungiyar sojojin aware na Rapid Support Forces (RSF), wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane kuma ya tilasta wa miliyoyin mutane guduwa daga gidajensu.

Rumbun Labarai
Shugaban Nijar ya ziyarci Aljeriya, lamarin da ya nuna ƙarshen tsamin dangantaka tsakanin ƙasashen
Trump ya bar ƙofar Iran a bude, kuma Netanyahu ba zai iya rufe ta ba
Yadda 'yan Nijeriya suka fusata kan matakin Amurka na saka wa Kwankwaso takunkumi
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tsarin aika sakamakon zabe kai-tsaye ta intanet
Taƙaddama a kan gyaran dokar zaɓe ta Nijeriya
Ghana ta yi wa jakadanta a Nijeriya kiranye kan zargin maguɗin zaɓe
Iran ta ce ta shiga tattaunawar Oman da Amurka da 'kyakkyawar niyya'
Greenland ba hajar sayarwa ba ce
Yayin da duniya ta koma kasuwar buƙatar diflomasiyya, wai zai tsaya wa ƙasashe marasa ƙarfi a 2026?
Amurka ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza
Alkawarin dala miliyan 150 zai sake gina Aleppo da yaƙi ya lalata
Yadda 'nadamar zalunci' ke janyo rushewar lafiyar ƙwaƙwalwa a rundunar sojin Isra’ila
Me ya sa Trump da masu sharhi da ke da ra’ayin rikau ke sa ido kan al’ummar Somalia da ke Minnesota?
Shugaban Nijar Tiani ya karɓi shugaban Bilma bayan ya yi watanni 16 a hannun masu garkuwa da mutane
An daƙile harin RSF kan West Kordofan: Rundunar Sojin Sudan
Nijar ta ce ta fara kai uranium ɗinta kasuwar duniya
Trump ya ce Amurka za ta dakatar da hijirar 'yan cirani daga kasashe marasa arziki har abada
Gobarar Hong Kong: Adadin waɗanda suka mutu ya kai 128 yayin da aka shiga kwana uku a ƙoƙarin ceto
China ta yi gargaɗin 'murƙushe' katsalandan ɗin ƙetare kan shirin makami mai linzani na Japan
Yaƙin Sudan: Maye gurbin UAE da Turkiyya na iya ƙarfafa ƙoƙarin ƙasashe na samar da zaman lafiya