Saudiyya da Isra'ila za su Amurka don tattaunawa yayin da Trump ke tura jiragen yaƙi na ruwa Iran
Shugaban hukumar leƙen asirin Isra'ila zai yi wa Washington karin bayani kan yiwuwar kai hari Iran, yayin da jami'an Saudiyya ke neman mafita ta diflomasiyya don kauce wa yaki a yankin, kamar yadda kafar Axios ta rawaito.
Jami'an tsaro da na hukumar leken asiri daga Isra'ila da Saudiyya za su ziyarci Amurka a wannan makon don tattaunawa kan Iran a daidai lokacin da sojojin Amurka ke ci gaba da isa yankin, kamar yadda shafin labarai na Axios ya ruwaito.
Janar Shlomi Binder, shugaban leken asirin sojojin Isra'ila, ya gudanar da wasu jerin zaman shawarwari na manyan jami'ai a ranar Talata da Laraba tare da manyan shugabannin Pentagon, CIA da Fadar White House, in ji Axios, yana mai ambato wasu jami'an Amurka biyu.
Ana sa ran tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan ba da takamaiman bayanan sirri da gwamnatin Trump ta nema, gami da bayanai kan yiwuwar kai hari a Iran.
A ɓangare guda kuma, ana sa ran Ministan Tsaron Saudiyya Yarima Khalid bin Salman zai jaddada hanyoyin diflomasiyya a yayin ganawarsa ta ranar Alhamis da Juma'a da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio da wakilin Amurka Steve Witkoff da kuma jami'an Pentagon.
Ma'aikatar Tsaron Saudiyya ta ce Yarima Khalid da tawagar da ta yi masa rakiya sun isa Washington a ziyara da ta mayar da hankali kan "tattaunawa kan dangantakar da ke tsakanin ƙasashen biyu masu ƙawance da kuma hanyoyin da za su ƙarfafa juna ,tare da taɓo batutuwan da suka shafi ƙasashen biyu."
Ƙaruwar ayyukan diflomasiyya
Saudiyya, wacce ke a tsakiya wajen isar da saƙonni tsakanin Washington da Tehran, ta ce a baya ba ta yarda Amurka ta yi amfani da sararin samaniyarta wajen kai hari a Iran ba.
Hakan na zuwa ne yayin da Amurka ta aika tawagar jiragen sama ta USS Abraham Lincoln don kammala isowar manyan jiragen "rundunar sojin ruwa na ƙasar" da Shugaba Donald Trump ya yi iƙirarin sun "fi girma" idan aka kwantata da rundunar da aka tura Venezuela kwanan nan.
"Umarnin a yanzu shi ne a shirya," in ji wani jami'in Amurka, yana mai nuna cewa shugaban Trump na gab da yanke shawara ta ƙarshe kan matakin soji da za a dauka.
Trump ya buƙaci Iran ta cim ma yarjejeniya kan shirin nukiliyarta kafin lokaci ya kure, yana mai gargaɗin cewa a wannan karon hari zai "fi muni."
Amurka ta kai hari kan wuraren nukiliyar Iran har guda uku a watan Yuni a lokacin yaƙin kwanaki 12 da Tehran ke yi da Isra'ila,
Iran ta ce shirin nukiliyarta na farar hula na dalilan zaman lafiya ne, amma ƙasashen yamma sun kafa sun tsare kan cewa tana ƙera makamin nukiliya ne.
Shirin makami mai linzami na Iran dai ya fusata Amurka da ƙawarta Isra'ila.