Ana gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Djibouti inda Guelleh da ke mulki ke neman wa'adi na shida
Shugaba Guelleh da ke mulki a ƙasar da ke da kimanin mutum miliyan ɗaya yanzu ya shafe fiye da shekara ashirin yana mulki.
Masu kaɗa ƙuri’a a ƙaramar ƙasar da ke yankin Kusurwar Afirka ta Djibouti suna zaɓe ranar Jumma’a, inda ake sa rai Shugaba Ismaïl Omar Guelleh da ya daɗe a kan mulki zai samu nasarar yin wa’adi na shida.
Hakan na faruwa ne bayan ‘yanmajalisar dokokin ƙasar sun cire wa’adin mulki ga shugaban ƙasar daga kundin tsarin mulki a shekarar da ta gabata.
Guelleh, mai shekara 78, ya shafe fiye da shekara ashirin yana mulkin ƙasar mai mutane kimanin miliyan 1.
Sakamakon zaɓen shekarar 2021 ya nuna cewa ya yi nasara da kashi 99 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa.
Yana fuskantar mutum ɗaya ne da ke ƙalubalantarsa, Mohamed Farah Samatar, wani tsohon ɗan jam’iyya mai mulki, a fafatawar da masu sharhi ke ganin babu hamayya mai ƙarfi.
Jam’iyyun hamayya suna yawan ƙaurace wa zaɓuka, inda suke ishara ga taƙaita ‘yancin siyasa, yayin da hukumomi ke cewa an samu zaman lafiya a wannan yanki mai cike da tashin hankali.
Guelleh ya gaji kawunsa, tsohon Shugaba Hassan Gouled Aptidon, a shekarar 1999, lamarin da ya tsawaita tsarin da iyalin ke jagoranta da ya shafe gomman shekaru yana juya akalar siyasar ƙasar.
Muhimmanci ga yanki
Djibouti na da sansanonin soji na ƙasashen waje, ciki har da na Amurka da China da Faransa da kuma Japan, lamarin da ke nuna muhimmancinta a hanyar jigilar kayayyaki ta ruwa ta duniya a hanyar da ta haɗa Bahar Ahmar da gaɓar tekun Aden.
Kuɗaɗen shiga daga waɗannan tsare-tsaren, tare da hidimar tashar jirgin ruwa ga ƙasar Ethiopia mai maƙwabtaka, na taimaka wa tattalin arzikin ƙasar.
Amma wannan tsarin ya sa matsalolin ƙetare ka iya shafar Djibouti. Ta dogara sosai kan amfanin da ƙasar Ethiopia ke yi da tashar jiragen samanta, yayin da tsaiko na duniya — ciki har da rashin tsaron jigila ta hanyar tekun bahar ahmar — suke barazana ga kuɗaɗen shiga.
Lamarin da ke ƙara gogayya ta yanki da kuma dogara kan bashi, musamman na China, sun kuma ƙara rashin tabbas na tsawon lokaci.
Masu sa ido a zaɓe na yanki daga ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) da ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen gabashin Afirka (IGAD) suna sa ido kan zaɓen.