| Hausa
TURKIYYA
1 minti karatu
Matar shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta tuna da ranar murƙushe yunƙurin juyin mulkin 15 ga Yuli
Emine Erdogan ta ce murƙushe yunƙurin juyin mulkin ‘wata jajircewa ce da ta bijiro bisa kishin ƙasa da kuma ƙwazo marasa iyaka’.
Matar shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta tuna da ranar murƙushe yunƙurin juyin mulkin 15 ga Yuli
Matar shugaban Turkiyya Emine Erdogan ta halarci bikin buɗe ɗakin karatu a wata makaranta a Istanbul ranar 14 ga Fabariru, 2026.

Matar shugaban ƙasar Turkiyya Emine Erdogan ranar Laraba ta ce yunƙurin juyin mulkin ranar 15 ga watan Yulin 2016, wanda aka murƙushe wata alama ce ta jajircewar ƙasar Turkiyya da yin tsayin-daka, inda ta jinjina wa waɗanda suka kare dimokuraɗiyya.

A wani saƙo da ta wallafa a shafin sada zumunta na Turkiyya NSosyal domin tunawa da Ranar Dimokuraɗiyya da Haɗin Kan Ƙasa wadda aka yi wa take da cewa #NasaraTamuCe wato #VictoryIsOurs a Turancin Ingilishi, Emine Erdogan ta ce ranar 15 ga Yuli "wani suna ne na jarumta da ta bijiro bisa kishin ƙasa da ƙwazo marasa iyaka."

"A wancan daren, gwarazanmu, waɗanda suka kasance haske maganin duhu, suna cikin zukatanmu kuma sun zama wata murya ta jajircewar ƙasa da kuma kare martaba da ‘yancinmu," in ji ta.

Matar shugaban Turkiyya ta ce fafutuka da sadaukarwar da aka yi wajen kare dimokuraɗiyya za su kasance “a zukatan ƙasarmu har abada."

Kazala ta jinjina wa waɗanda suka rasa rayukansu da waɗanda aka jikkata a lokacin yunƙurin juyin mulkin.

“Ina jinjina wa shahidai na ranar 15 ga Yuli tare da tunawa da gwarazan dakarunmu da yi musu godiya,” a cewarta.

Rumbun Labarai
An fara gasar baje-kolin jiragen sama marasa matuka ta TEKONOFEST a garin Sirnak na Turkiyya
Erdogan zai kai ziyara Saudiyya don tattaunawa da Mohammed bin Salman da Firaministan Pakistan
Shugaban sadarwa na Turkiyya ya ce Isra'ila na yi wa yunƙurin zaman lafiya na Gaza zagon ƙasa
Turkiyya ta kama ɗanta'addan FETO da ake nema bisa yunƙurin kashe Shugaba Erdogan a shekarar 2016
Turkiyya ta yi fice a Gasar Duniya ta Rubutu a Kwamfuta da kambi 36
Turkiyya da Nijeriya sun ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa kan ƙera jiragen ruwa
Shugaba Erdogan ya taya tawagar Sultans of Net ta Turkiyya murnar lashe gasar ƙwallon raga ta mata
Shugaba Erdogan ya yi taron cika shekaru shida da sake bude Hagia Sophia don Ibadar Musulmai
Ayyukan ‘yan kama-wuri-zauna na Isra’ila na barazana ga ƙoƙarin zaman lafiya a Ƙudus: Turkiyya
Turkiyya ta yi kira ga Amurka da Iran su koma kan yarjejeniya, su kuma yi aiki tare da Qatar
Girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 5 ta auka wa gabashin Turkiyya
Ga yadda Turkiyya ke son hana ‘yan ƙasa da shekaru 18 shan taba sigari
Dangantakar Turkiyya da Afirka da yaƙi da FETÖ bayan yunƙurin juyin mulkin 15 ga Yuli da aka daƙile
Daƙile yunƙurin juyin mulki na 2016 ya 'bayyana 'yancin kai' na ƙarni ga Turkiyya, in ji  Erdogan
Turkiyya na juyayin cika shekaru 10 da yunƙurin juyin mulki na ranar 15 ga Yuli da bai yi nasara ba
Turkiyya ta umarci makarantu su goge hotunan ɗaliban da aka wallafa ba tare da izinin iyaye ba
Jami’an leƙen asiri na Turkiyya sun kama wani babban jami’in Daesh a Syria
Manufofi da gwamnatin Netanyahu 'nauyi' ne ga Isra'ila da yankin da tsaron duniya: Ministan Turkiyya
Emine Erdogan ta karbi bakuncin matan shugabannin NATO don tattaunawa kan yara, fasaha da tsaro
Shugaba Erdogan ya ce taron NATO a Ankara ‘nasara ce ta tarihi’